ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai 2,199 Sun Amfana Da Tallafin Karatu A Kananan Hukumomin Musawa Da Matazu A Katsina

by Zaharadden Umar and Sulaiman
9 months ago
Tallafin karatu

Dalibai 2,199 daga suka fito daga kananan hukumomin Musawa da Matazu suka amfana da tallafin karatun dan majalisar wakiltar kananan hukumomin Musawa Hon. Abdullahi Aliyu.

Tallafin na da nufin ragewa dalibai kudin rijista a daidai lokacin da ake fama da matsalolin rayuwa na yau da kullum musamman a yankunan karkara.

  • Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Naira Biliyan 878 A Matsayin Kasafin 2026
  • Sin Ta Kasance Mai Goyon Bayan Kasashen Afirka Wajen Zamanantar Da Kansu  

Haka kuma daliban sun hada da masu karatu a kwalejin kimiyya da fasaha ta Katsina Poly da kwalejin gwamnatin tarayya ta F.C.E Katsina da Jami’ar Umaru Musa Yar’adua da kwalejin kimiyya ta ICT Katsina

ADVERTISEMENT

Bada tallafin ya gudana a karkashin kwamitin ilmin dan majalisar wanda tsohon mataimakin gwamna Alhaji Tukur Ahmad Jikamshi ke jagoranta.

Da yake jawabi a wajen taron raba tallafin dan majalisar wakilai na kananan hukumomin Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu Dujiman Katsina ya bayyana dalibai 1,029 sun fito ne daga jami’o’i wanda kowane zai samu tallafin Naira ₦30, 000 wanda kudin suka kama miliyan 30,870,000

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Ya kuma kara da cewa kimanin dalibai 1,170 sun fito ne da kwalejin gwamnatin tarayya da kuma na jihohi inda kowa zai samu tallafin Naira ₦20,000 inda za a ba su Naira miliyan 23,400 baki dayan su.

Hon. Abdullahi Aliyu Dujiman Katsina ya ce an kashe kimanin naira miliyan 54,270,000 a matsayin tallafin kudin rijista a makarantun gaba da sikandire ga mutane 2,199 da suka fito daga kananan hukumomin Musawa da Matazu

“Yanzu mun maida hankalinmu akan shirye-shirye da tsare-tsaren samar da makoma mai kyau ga matasa acikin al’umma musamman abinda ya shafi harkar ilmi da kiwon lafiya da sauran su ‘ inji shi

Shugaban kwamitin ma’aikatar cikin gida, ya kara da cewa zai cigaba da riɓanya kokarin sa na ganin an inganta rayuwar matasa ta hanyar sama musu aikin yi da tallafi domin yin sana’a domin dogaro da kan su.

Haka kuma ya yi alkawarin samarwa matasa 420 da suka fito daga kananan hukumomin Musawa da Matazu aikin yi domin rage zaman kwashe wando a tsakanin matasa.

Idan za a iya tunawa dan majalisar ta samarwa matasa aikin yi a hukumar kashe gobara ta kasa da Asibitin koyarwa ta Katsina da ‘yan sanda da sojoji da hukumar shige da fice ta kasa (immigration) da hukumar tsaro ta sibil difans.

A cewar sa, nan bada jimawa ba, zai raba mashina guda 500 ga matasa da suka fito daga kananan hukumomin Musawa da Matazu domin a samu saukin zirga-zirga a wannan yankuna.

” Babban abinda ke gabana yanzu shi ne matasa inasan in ga rayuwar matasa ta canza daga halin da suka tsinci kansu a wannan lokaci da ake fuskantar matsalolin rayuwa na yau da kullum” inji shi

Tunda farko da yake jawabi shugaban karamar hukumar Musawa Hon. Aliyu Idris Gingin ya bayyana tallafin a matsayin wani kaɓakin arziki da zai taimakawa harkar ilmi karkashin inuwar dimokuradiyyar

Ya kuma kara da cewa hakan zai taimaka wa daliban wajen bunkasa ilimin su sannan Dujiman Katsina ya kama hanyar da gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Radda ya dora gwamnatin sa akan ke nan.

 

Tallafin karatu
Zaharadden Umar
+ posts Bio
    This author does not have any more posts.
Tallafin karatu
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.