Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi ta Tarayya a Jihar Kano, Abubakar Kabir Abubakar, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da kuma goyon bayan shirin kafa sabon asibitin koyarwa a Ƙaramar Hukumar Bichi.
Abubakar, wanda kuma shi ne Shugaban Kwamitin Kasafin Kuɗi na Majalisar Wakilai, ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin ƙaddamar da ma’aikatan lafiya 120 na wucin gadi da Gidauniyar Kabir Abubakar Bichi ta ɗauka aiki domin tura su cibiyoyin kula da lafiya na matakin farko a faɗin ƙaramar hukumar.
Taron ya samu halartar Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dakta Abubakar Labaran Yusuf, da sauran manyan baƙi.
Ɗan majalisar ya ce ana ci gaba da tattaunawa domin samun amincewa ta ƙarshe daga Gwamnatin Tarayya kan kafa asibitin koyarwar, tare da saka aikin cikin kasafin kuɗin shekarar 2026.
Ya ce, “Kwanan nan na halarci tarurruka kan bunƙasa ilimi da harkokin lafiya. Kamar yadda kuka sani, muna da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano, kuma ina tabbatar muku cewa muna aiki kafaɗa da kafaɗa da Ministan Lafiya da Babban Daraktan Asibitin Koyarwa na Aminu Kano domin tabbatar da kafa sabon asibitin koyarwa a Bichi.”













