Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bayyana a yau Litinin cewa, a shirye Sin take ta kara karfafa dangantaka da hadin gwiwa da bangarori da dama da Brazil.
Shugaban ya bayyana haka ne yayin zantawa da takwaransa na Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ta wayar tarho, inda ya bukaci bangarorin biyu su kara taka rawar gani wajen inganta tsarin shugabancin duniya da daukaka adalci da daidaito a duniya.
Xi Jinping ya kara da cewa, ya kamata Sin da Brazil su hada hannu wajen inganta ci gaban hadin kan kasashen BRICS. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)
ADVERTISEMENT
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
-
CGTN Hausahttps://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/














