Mahukuntan Kwalejin Fasaha ta Jihar Kogi, Lokoja, sun dakatar da malamai bakwai daga aiki bisa zargin cin zarafin ɗalibai ta hanyar neman lalata domin ba su maki, da kuma sayar da takardun karatu da littattafai ba tare da izini ba.
Mai magana da yawun kwalejin, John Onimisi, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a Lokoja.
A cewar sanarwar, an dakatar da malamai shida a ranar Laraba, 22 ga Yuli, 2026, saboda zargin sayar da takardun karatu da littattafai ba tare da amincewar hukuma ba, yayin da aka dakatar da wani malami guda bisa zargin cin zarafin wata ɗaliba ta hanyar neman lalata da ita.
Dakatarwar ta biyo bayan ƙara yawaitar zarge-zargen neman lalata da ɗalibai domin ba su maki, ayyukan ƙungiyoyin asiri, da sauran halayen rashin ɗa’a da ake zargin suna faruwa a cikin kwalejin.
Majiyoyin da ke da masaniya kan lamarin sun yi zargin cewa wasu malamai na neman lalata ko kuɗi daga ɗalibai mata domin ba su maki na cin jarabawa, yayin da kuma ake zargin ayyukan ƙungiyoyin asiri sun sake bayyana a harabar kwalejin.













