Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta kammala aikin rajistar masu kaɗa ƙuri’a (CVR) a faɗin ƙasar ranar Lahadi, gabanin babban zaɓen shekarar 2027, tare da buƙatar waɗanda suka yi rajista su jira lokacin da za a baje kundin sunayen masu zaɓe domin tantance bayanansu.
Hukumar ta kuma tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa duk wata ƙuri’a ingantacciya da aka kaɗa za ta yi tasiri a zaɓukan da ke tafe.
INEC ta sanya ranar 26 ga Yulin 2026 a matsayin ranar ƙarshe ta aikin rajistar, wanda ya haɗa da sabbin rajista, sauya wurin rajista, gyaran bayanan masu zaɓe da kuma maye gurbin katin zaɓe na dindindin (PVC) da ya ɓace ko ya lalace.
A wani ɓangare kuma, Shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa hukumar na ci gaba da jajircewa wajen gudanar da sahihin zaɓe, inda kowace ƙuri’a ingantacciya za ta kasance mai tasiri.
Da yake jawabi yayin wata ziyarar girmamawa da ya kai wa tsohon Shugaban Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Zaman Lafiya na Ƙasa, Janar Abdulsalami Abubakar (mai ritaya), a Minna, Jihar Neja, Amupitan ya ce duk da ƙalubalen da hukumar ke fuskanta, za ta tabbatar da cewa ra’ayin masu zaɓe ne ya yi rinjaye.
A nasa jawabin, Janar Abdulsalami ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su bai wa INEC cikakken goyon baya wajen gudanar da sahihin zaɓe, yana mai cewa ci gaba da amincewar jama’a da tsarin zaɓe na da matuƙar muhimmanci ga dorewar dimokuraɗiyyar ƙasar.













