Aƙalla mutane 30, ciki har da mata da ƙananan yara, sun rasa rayukansu bayan wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari ƙauyen Naridom da ke Masarautar Chawai, a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna.
Rahotanni sun ce maharan sun mamaye ƙauyen ne da tsakar daren Litinin, tsakanin ƙarfe 12:00 zuwa 1:00 na dare, inda suka riƙa harbe-harbe kan mazauna yankin har kusan sa’o’i uku, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, ƙone gidaje da shaguna, tare da jefa al’umma cikin firgici.
Wani mazaunin ƙauyen, Barnabas Musa, ya shaida wa LEADERSHIP cewa harin ya fara ne tsakar dare, kuma ya ci gaba har zuwa misalin ƙarfe 3:00 na asuba, yayin da mazauna yankin ke ta neman agajin jami’an tsaro.
A cewarsa, sama da mutane 30, ciki har da mata da yara, aka kashe a harin, yayin da maharan suka kuma ƙone shaguna huɗu da gidaje biyu kafin su tsere.













