Jam’iyyar ADC ta buƙaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayyana irin ci gaban da aka samu wajen ceto mazauna 176 na ƙauyen Woro da ke ƙaramar hukumar Kaiama a Jihar Kwara, waɗanda aka sace tun ranar 3 ga Fabrairu, 2026. Jam’iyyar ta ce ya kamata gwamnati ta ba su kulawa irin wadda ta bai wa waɗanda aka ceto a Jihar Oyo.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na Ƙasa na jam’iyyar, Mallam Bolaji Abdullahi, ya sanya wa hannu, ADC ta ce mutanen Kaiama sun shafe sama da kwanaki 170 a hannun masu garkuwa da mutane. Ta kuma tunawa da zanga-zangar lumana da mazauna yankin suka yi domin neman a ceto ‘yan uwansu.
Jam’iyyar ta kuma nuna damuwa kan ci gaba da taɓarɓarewar tsaro, inda ta ambaci sace sama da mutum 40, galibinsu mata da yara, a Jihar Zamfara, da hare-haren da aka kai a Binuwe, da kuma sace Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruku Hassan Bunza. Haka kuma ta ce hare-haren da ake ci gaba da kai wa a Borno na nuna cewa matsalar tsaro har yanzu tana addabar miliyoyin ‘yan Nijeriya.
ADC ta buƙaci gwamnatin tarayya ta riƙa ba da cikakken bayani kan ƙoƙarin ceto waɗanda ke hannun masu garkuwa da mutane, maimakon yawan alkawuran da ba sa nuna sakamako. Jam’iyyar ta jaddada cewa shugabanci nagari yana nufin tabbatar da cewa babu wani ɗan Nijeriya da aka manta da shi, ba tare da la’akari da inda ya fito ba ko irin shaharar lamarinsa.













