• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari’a

by Abubakar Sulaiman
11 months ago
in Labarai
0
Ganduje Ya Buƙaci A Haɗa Hannu don Ƙarfafa Fannin Shari’a
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dr. Abdullahi Ganduje, Shugaban Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na ƙasa, ya yi kira ga haɗa hannu tsakanin shugabannin siyasa domin ƙarfafa ɓangaren shari’a, da kare doka da oda, da kuma kare tsarin dimokuraɗiyya a Nijeriya.

Da yake jawabi a zaman tattaunawa na farko na ƙungiyar shawarar Jam’iyyu (IPAC) da aka gudanar a Abuja mai taken “Matsayin Shari’a wajen ɗorewar Dimokuraɗiyya a Nijeriya,” Ganduje ya jaddada muhimmancin rawar da ɓangaren shari’a ke takawa wajen gina dimokuraɗiyyar ƙasa.

  • Gwamnan Kano Ya Kwace Filayen Makarantun Da Ganduje Ya Cefarnar
  • Za A Sake Maka Ganduje A Kotu Kan Badaƙalar Naira Biliyan 57.4

Ganduje ya amince da ƙalubalen da ɓangaren shari’a ke fuskanta, wanda ya haɗa da rashin wadataccen kuɗi, da jinkirin gudanar da shari’a, da kuma buƙatar ‘yancin ɓangaren shari’a. Ya bayyana cewa duk da waɗannan ƙalubalen, akwai damarmakin yin gyare-gyare da za su ƙara inganta rawar da ɓangaren shari’a ke takawa wajen ɗorewar dimokuraɗiyya. Ya yi kira da a tabbatar da cewa ɓangaren shari’a ya kasance mai cin gashin kansa kuma ba tare da tasiri daga waje ba.

Sanarwar karshe ta zaman tattaunawar ta buƙaci kotunan Nijeriya da su duba sosai kan ƙa’idojin shari’ar zaɓe da ka iya taimakawa wajen yin magudi da kuma ƙaƙaba ‘yan takarar da aka ki su a zabe.

Mahalarta zaman tattaunawar sun buƙaci a yi gyare-gyaren da za su fifita tanade-tanaden kundin tsarin mulki, da zamanantar da amfani da shaidu na lantarki, tare da sanya tsauraran ƙa’idoji kan Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) game da tura sakamakon zabe.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Haka kuma sun shawarci ɓangaren shari’a da ya nisanci tasirin siyasa sosai, tare da yin tsarin ɗaukar alƙalan kotu bisa gaskiya da cancanta domin tabbatar da mutuncin ɓangaren shari’a.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GandujeJudiciaryLegislature
ShareTweetSendShare
Previous Post

Aikin Hajjin 2024: Saudiyya Ta Karrama Jihar Sakkwato Da Babbar Lambar Yabo

Next Post

Ana Tuhumar Mutum 632 Da Laifin Sata Da Barnata Kaya A Kano

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

12 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

15 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

17 hours ago
Next Post
Ana Tuhumar Mutum 632 Da Laifin Sata Da Barnata Kaya A Kano

Ana Tuhumar Mutum 632 Da Laifin Sata Da Barnata Kaya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.