ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Girgizar Kasa: Shugaban Kasar Myanmar Ya Mika Godiya Ga Tawagar Likitocin Yunnan Ta Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Myanmar

Shugaban majalisar gudanarwar kasar Myanmar, babban janar Min Aung Hlaing, ya mika godiyarsa a yau Lahadi ga mambobin kungiyar likitoci masu aikin ceto ta Yunnan ta kasar Sin bisa taimakon da suka bayar a kan lokaci, bayan wata girgizar kasa mai karfi ta afku a kasar ta Myanmar a ranar Jumma’ar da ta gabata. 

Shugaban na Myanmar ya ziyarci asibitin Ottara Thiri mai zaman kansa da ke Nay Pyi Taw, babban birnin kasar Myanmar a yau Lahadin, inda ya gode wa tawagar masu aikin ceton ta kasar Sin, wacce ta garzaya yankin da abin ya shafa a farkon lokaci domin kai dauki.

  • Sin Da Jamhuriyar Congo Za Su Karfafa Raya Hadin Gwiwar Sin Da Afrika
  • Masana’antar Shirya Fina-Finan Kagaggun Labaran Kimiyya Da Fasaha Ta Sin Ta Samu Yuan Biliyan 108.96 A 2024

Tawagar masu aikin ceton ta kasar Sin da ta fito daga lardin Yunnan da ke kudu maso yammacin kasar, tare da hadin gwiwar ma’aikatan ceto na Myanmar, sun ceto wani dattijo da ya makale a girgizar kasar da ta afku a Nay Pyi Taw da misalin karfe 05:00 na asubahin yau Lahadi.

ADVERTISEMENT

Mutumin dai ya shafe kusan sa’o’i 40 a makale a karkashin baraguzan ginin asibitin da ke birnin. Bayan aikin ceton gaggawa da aka yi cikin dare, mutumin shi ne na farko da tawagar kasar Sin ta ceto shi da rai, bayan da ta isa yankin da girgizar kasar ta shafa a Myanmar, ranar Asabar.

Tawagar ta Sin mai mambobi 37 ta garzaya yankin dauke da rantsattsun na’urorin gano mutane masu rai, da na’urorin da ke yin gargadi a kan girgizar kasa a kan kari, da wayoyin tauraron dan’adam, da na’urorin aiki masu tashi sama, da sauran na’urorin ceto domin gudanar da ayyukansu na ceto.

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

Akwai karin tawagogin ceto da dama na kasar Sin da suka shiga ayyukan ba da agaji tare da takwarorinsu na Myanmar.

Girgizar kasar mai karfin maki 7.7 ta afku a kasar ce da ke kudu maso gabashin Asiya, a ranar Jumma’ar da ta gabata. A jiya Asabar da dare, tawagar yada labarai ta majalisar gudanarwar kasar ta bayyana cewa, sama da mutum 1,700 ne suka mutu, kana sama da 3,400 suka jikkata, yayin da kuma kimanin 300 suka bace, a kakkarfar girgizar kasar da ta faru a kasar ta Myanmar.

A yinin yau Lahadi kuma, wani jirgin saman kamfanin China Eastern Airlines ya tashi daga Kunming, babban birnin lardin Yunnan na kudu maso yammacin kasar Sin, dauke da kayayyakin agaji kimanin tan 7.3 zuwa kasar Myanmar da girgizar kasa ta afka wa.

An nemo kayayyakin agajin ne tare da tattara su a birnin na Yunnan, wadanda suka hada da tufafi, da magunguna, da taliya, da tantuna da sauran kayayyakin masarufi da ake bukata yau da kullum. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Myanmar
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Myanmar
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Next Post
Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina

Mutane 9 Sun Mutu Sanadin Haɗarin Mota A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.