Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC), ta bayyana shakku kan rahoton lafiyar da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya gabatar domin neman beli, tare da yin kira ga kotu da ta gudanar da shari’ar cikin gaskiya da adalci.
A cikin wata sanarwa da Shugaban MURIC na Jihar Kano kuma Mai Kula da Jihohin Arewa da Abuja, Malam Hassan Sani Indabawa, ya fitar, ƙungiyar ta ce duk da cewa ta daɗe tana kare haƙƙin El-Rufai, ba za ta yi watsi da gaskiya da adalci ba.
MURIC ta ce buƙatar beli ta uku da lauyoyin El-Rufai suka gabatar ta dogara ne kan rashin lafiya, tare da rahoton lafiya da aka ce Asibitin Ƙasa da ke Abuja ne ya fitar.
Sai dai, ƙungiyar ta ce Babban Daraktan Asibitin, Farfesa Muhammad Raji Mahmud, ya musanta sahihancin rahoton, yana mai cewa ba a fitar da shi da izini ko sanin mahukuntan asibitin ba.
A cewar MURIC, wannan ne ya sa Babbar Kotun Jihar Kaduna ta yi watsi da buƙatar belin a ranar 29 ga watan Yuni, 2026.
Ƙungiyar ta ce idan bincike ya tabbatar da cewa an ƙirƙiri rahoton ne, hakan zai kasance abin damuwa matuƙa.
MURIC ta kuma ce tana neman a mutunta haƙƙin El-Rufai, ciki har da ba shi damar ganin iyalansa da kuma samun kulawar likitoci yayin da ake yin shari’ar.
A ƙarshe, ƙungiyar ta buƙaci kotu ta yanke hukunci bisa hujjoji masu inganci kawai, tare da kira ga lauyoyin El-Rufai su tabbatar da cewa duk takardun da suke gabatarwa sahihai ne.
Haka kuma ta yi kira ga ɓangaren shari’a da ya ci gaba da gudanar da aikinsa ba tare da son rai ko matsin lamba ba.













