Gwamnonin da aka zaba a zangon farko na jam’iyyar APC a yanzu haka suna wani taron sirri a Birnin Kebbi, babban birnin jihar Kebbi.
Taron wanda ya na kan gudana ayau Litinin, gwamnan jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, Kauran Gwandu ne ke karbar bakoncin Gwamnonin a fadar gwamnati da ke Birnin Kebbi.
Har yanzu dai ba a san abin da za a tattauna a taron ba saboda ba a bayyana cikakkun bayanai kan ajandarsu ba.
An tattaro cewa gwamnoni hudu ne kawai ba su halarci taron ba. Su ne gwamnonin jihohin Katsina da Neja da Ribas da Kuros Ribas.
“Dukkan gwamnoni hudu sun aika da uzurinsu na rashin halartar taron,” in ji wata majiya da ke kusa da taron.
Kamar dai lokacin da aka fara taron har yanzu ‘yan jarida a jihar ba su tantance takamaiman makasudin taron ba.
Sai dai ‘yan jarida na sa ran bayan kammala taron za a yi musu bayani kan makasudi, sakamako da kuma kudurorin taron.
“Za a sanar da ku da kyau game da makasudin da sakamakon taron bayan an kammala shi,” in ji wata majiya mai tushe.
Ana sa ran bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar a karshen taron.













