An kai kayayyakin taimakon jin kai na gaggawa na farko da gwamnatin Sin ta ba kasar Venezuela zuwa filin jirgin sama na kasa da kasa na Simon Bolivar na birnin Maiquetia da ke kusa da Caracas, babban birnin kasar Venezuela a jiya Litinin.
Ministan harkokin waje na Venezuela, Yvan Gil, da jakadan Sin a Venezuela, Lan Hu, sun kasance a filin jirgin don tarbar kayayyakin. Minista Gil ya ce, tun bayan da girgizar kasa mai karfi ta abka wa Venezuela, bangaren Sin yana ta tuntubar gwamnatin Venezuela akai-akai. Ya kara da cewa, wadannan kayayyakin taimakon sun hada da tantuna, janareto da sauransu, kuma suna da matukar muhimmanci ga mutanen da suka rasa gidajensu sakamakon bala’in, tare da nuna dangantakar abokantaka bisa manyan tsre-tsare a ko da yaushe cikin ko wane yanayi da ke tsakanin kasashen biyu, kamar yadda Hausawa ke cewa, Mahdi ka ture.
Baya ga haka kuma, ministan ya ci gaba da cewa, bayan aukuwar bala’in, Sinawa mazauna Venezuela da kamfanonin Sin dake kasar sun samar da taimako cikin gaggawa, kana sun shiga aikin ceto tun daga farkon lokacin da abin ya faru, don ba da kulawa ga mutanen da suka rasa matsugunansu, kuma an ga al’amura da dama na kirki masu ratsa zuciya. (Bilkisu Xin)














