ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Bas-bas 50 Ga Ƙungiyar Direbobi Ta Zamfara

by Sulaiman
3 weeks ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya miƙa sabbin motocin bas-bas guda 50 ga reshen Ƙungiyar Direbobi ta Ƙasa (NURTW) na jihar, a wani mataki da gwamnatin ta ce na inganta harkokin sufuri da bunƙasa tattalin arziki.

An gudanar da bikin miƙa motocin ne a ranar Laraba a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Gusau.

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa gwamnatin jihar ta samar da motocin ne a matsayin rance ƙarƙashin Tsarin Ba da Lamuni na Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnatin ta ƙara samar da motocin kashe gobara guda biyar domin ƙarfafa ayyukan kashe gobara a faɗin jihar.

Zamfara

Da yake jawabi yayin bikin, Gwamna Dauda Lawal ya ce shirin bayar da motocin a matsayin lamuni wani ɓangare ne na manufofin gwamnatinsa na inganta tsarin sufurin jama’a, ƙarfafa tattalin arziki da kuma tabbatar da ingantaccen kuma amintaccen sufuri ga al’ummar jihar.

LABARAI MASU NASABA

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Ya ce, an amince motocin za su kasance ƙarƙashin kulawar NURTW, inda ƙungiyar za ta taimaka wajen tantance waɗanda za su amfana, sa ido kan yadda ake amfani da motocin da kuma tabbatar da biyan kuɗin lamunin.

Gwamnan ya bayyana cewa kowace mota ta kai darajar Naira miliyan 27.39, amma gwamnatin jihar za ta ɗauki kashi 20 cikin 100 na kuɗin a matsayin tallafi.

A cewarsa, wannan tallafin ya kai Naira miliyan 5.478 kan kowace mota, yayin da wanda ya amfana zai biya Naira miliyan 21.912 cikin watanni 44 daga ranar karɓar motar.

Gwamna Lawal ya kuma ƙaddamar da motocin kashe gobara guda biyar da gwamnatin ta saya domin inganta aikin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Zamfara.

Zamfara

Ya ce, gobara na iya lalata gidaje, shaguna da hanyoyin samun abinci cikin ɗan ƙanƙanin lokaci, don haka sabbin motocin da aka tanada da kayan aiki na zamani za su taimaka wajen hanzarta kai ɗauki a kowane lungu da saƙo na jihar.

Ya buƙaci jami’an hukumar kashe gobara su ci gaba da horas da ma’aikatansu, wayar da kan jama’a kan hanyoyin kare kai daga gobara, tare da tabbatar da cewa motocin da kayan aikin suna cikin kyakkyawan yanayin aiki a kowane lokaci.

Gwamnan ya jaddada cewa dukkan motocin da aka raba mallakin al’ummar Jihar Zamfara ne, yana mai umartar dukkan ma’aikatu, hukumomi da masu cin gajiyar shirin da su riƙa gabatar da rahoton yadda ake amfani da kadarorin da kuma yadda ake kula da su duk bayan wata uku.

Zamfara

Ya kuma yi gargaɗin cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci lalata kadarorin gwamnati, amfani da su ba bisa ƙa’ida ba ko karkatar da su zuwa wata manufa daban ba.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI
  • Sulaiman
    Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya
  • Sulaiman
    Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
  • Sulaiman
    Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

MASU ALAKA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Labarai

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari
Labarai

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
Next Post
NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

Jadawalin INEC:Kotun Daukaka Kara Ta Kassara Fatan Jam’iyyu Da ‘Yan Siyasa

July 24, 2026
An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

An Zartas Da Sanarwar Chengdu A Taron Ministocin Kungiyar APEC Kan Harkar Raya Fasahohin Dijital Da AI

July 24, 2026
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso

Jam’iyyar NDC Ta Shirya Tsaf Domin Kafa Gwamnati A 2027 —Kwankwaso

July 24, 2026
Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

Sin Ta Kara Kamfanoni 14 Na Tarayyar Turai Cikin Jerin Wadanda Aka Hana Fitar Masu Da Kaya

July 24, 2026
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Kyamar Baki: Shettima Ya Ja Kunnen Gwamnatin Afirka Ta Kudu

July 24, 2026
Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

Yadda Kasar Sin Ta Samar Da Ci Gaba Na Bai Daya

July 24, 2026
Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

Hatsin Da Kasar Sin Ta Girbe Da Lokacin Zafin Bana Ya Zarce Tan Miliyan 150

July 24, 2026
Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

Wani Dalilin Da Ya Sa Al’Ummar Afirka Ke Kaunar Kasar Sin Shi Ne Yadda Take Kokarin Zuba Musu Jari

July 24, 2026
NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

NLC Ta Yi Barazanar Daukar Matakin Yajin Aiki Kan Albashi Mafi Karanci

July 24, 2026
Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

Sin Tana Son More Damammakin Fasahar AI a Maimakon Babakere a Wannan Bangare Da Kasashen Yamma Suka Dade Suna Yi

July 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.