ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Bas-bas 50 Ga Ƙungiyar Direbobi Ta Zamfara

by Sulaiman
2 days ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya miƙa sabbin motocin bas-bas guda 50 ga reshen Ƙungiyar Direbobi ta Ƙasa (NURTW) na jihar, a wani mataki da gwamnatin ta ce na inganta harkokin sufuri da bunƙasa tattalin arziki.

An gudanar da bikin miƙa motocin ne a ranar Laraba a Gidan Gwamnatin Jihar da ke Gusau.

Mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cikin wata sanarwa cewa gwamnatin jihar ta samar da motocin ne a matsayin rance ƙarƙashin Tsarin Ba da Lamuni na Jihar Zamfara.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta kuma bayyana cewa gwamnatin ta ƙara samar da motocin kashe gobara guda biyar domin ƙarfafa ayyukan kashe gobara a faɗin jihar.

Zamfara

Da yake jawabi yayin bikin, Gwamna Dauda Lawal ya ce shirin bayar da motocin a matsayin lamuni wani ɓangare ne na manufofin gwamnatinsa na inganta tsarin sufurin jama’a, ƙarfafa tattalin arziki da kuma tabbatar da ingantaccen kuma amintaccen sufuri ga al’ummar jihar.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Ya ce, an amince motocin za su kasance ƙarƙashin kulawar NURTW, inda ƙungiyar za ta taimaka wajen tantance waɗanda za su amfana, sa ido kan yadda ake amfani da motocin da kuma tabbatar da biyan kuɗin lamunin.

Gwamnan ya bayyana cewa kowace mota ta kai darajar Naira miliyan 27.39, amma gwamnatin jihar za ta ɗauki kashi 20 cikin 100 na kuɗin a matsayin tallafi.

A cewarsa, wannan tallafin ya kai Naira miliyan 5.478 kan kowace mota, yayin da wanda ya amfana zai biya Naira miliyan 21.912 cikin watanni 44 daga ranar karɓar motar.

Gwamna Lawal ya kuma ƙaddamar da motocin kashe gobara guda biyar da gwamnatin ta saya domin inganta aikin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Zamfara.

Zamfara

Ya ce, gobara na iya lalata gidaje, shaguna da hanyoyin samun abinci cikin ɗan ƙanƙanin lokaci, don haka sabbin motocin da aka tanada da kayan aiki na zamani za su taimaka wajen hanzarta kai ɗauki a kowane lungu da saƙo na jihar.

Ya buƙaci jami’an hukumar kashe gobara su ci gaba da horas da ma’aikatansu, wayar da kan jama’a kan hanyoyin kare kai daga gobara, tare da tabbatar da cewa motocin da kayan aikin suna cikin kyakkyawan yanayin aiki a kowane lokaci.

Gwamnan ya jaddada cewa dukkan motocin da aka raba mallakin al’ummar Jihar Zamfara ne, yana mai umartar dukkan ma’aikatu, hukumomi da masu cin gajiyar shirin da su riƙa gabatar da rahoton yadda ake amfani da kadarorin da kuma yadda ake kula da su duk bayan wata uku.

Zamfara

Ya kuma yi gargaɗin cewa gwamnatinsa ba za ta lamunci lalata kadarorin gwamnati, amfani da su ba bisa ƙa’ida ba ko karkatar da su zuwa wata manufa daban ba.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran
  • Sulaiman
    Sin Ta Soki Abin Da Amurka Da Tarayyar Turai Ke Kira Da Wai ‘Damuwa Kan Sabuwar Dokar Kabilu’
  • Sulaiman
    CGTN Ta Gudanar Da Nazari Kan Yadda Jama’Ar Duniya Ke Kallon Amurka

MASU ALAKA

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
Labarai

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
Labarai

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
Labarai

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Next Post
NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

NSC Ta Ƙaddamar Da Shugabannin Wasannin Masu Buƙata Ta Musamman

LABARAI MASU NASABA

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026
Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

Gwamnan Katsina Ya Kai Ziyarar Duba Aikin Cibiyar Gyaran Motoci Mai Amfani Da Hasken Rana

July 4, 2026
Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

Yadda Ayyukan Titunan Gwamnan Kaduna Suka Farfaɗo Da Ilimi Da Kiwon Lafiya Da Noma A Sabon Gari

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Uwargidan Shugaban Ƙasa Ta Ƙaddamar Da Muhimman Ayyukan Ci Gaba A Jihar Jigawa

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.