ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
7 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar Tsafe, a wani bangare na shirinsa na farfaɗo da inganta muhimman cibiyoyin jama’a a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kona Ofishin ‘Yansanda, Coci Tare Da Garkuwa Da Waus A Neja
  • Karuwar Mace-mace A Asibitocinmu Sakamakon Sakacin Jami’an Lafiya

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sabunta tashar mota ta zamani, gyaran kasuwa, gyaran makaranta, sabuntawa da kuma samar da kayayyakin aiki a babban asibitin Tsafe, da kuma gyaran fadar sarkin Tsafe.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

A cewar sanarwar, waɗannan ayyuka suna taka muhimmiyar rawa a rayuwar al’umma, musamman a bangarorin shugabanci, kiwon lafiya, ilimi, kasuwanci da zirga-zirga, tare da ƙara danƙon zumunci da jin cewa jama’a na da hannu a ci gaban yankinsu.

Lawal

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya ce sabunta fadar sarkin Tsafe alama ce ta girmama al’ada da kuma tabbatar da darajar masarautu a tsarin shugabanci na ƙasa. Ya ce sarakuna na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, warware rikice-rikice da kuma haɗa kan al’umma.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da masarautu a matsayin abokan hulɗa wajen sake gina Zamfara da dawo da martabar ta.

 

A bangaren ilimi da bunƙasa jarin ɗan Adam, ya bayyana cewa inganta Kwalejin Kiwon Lafiya ta Tsafe na nufin zuba jari ne a kan makomar ma’aikatan lafiya da za su yi hidima ga al’umma. A cewarsa, gyaran muhalli da kayan aikin makarantar zai ƙara inganta kwarewa da kwarin gwiwar ɗalibai.

 

Dangane da harkar lafiya kuwa, Gwamna Lawal ya ce sabunta babban asibitin Tsafe da samar masa da kayan aiki na zamani zai inganta ayyukan jinya, sauƙaƙa wa marasa lafiya da kuma taimaka wa ma’aikatan lafiya wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

 

Ya kuma jaddada cewa kasuwa da tashar mota na daga cikin ginshiƙan tattalin arzikin yankin, domin su ne ke haɗa manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da sauran jama’a. Sabunta waɗannan wurare, in ji shi, zai inganta tsari, tsaro da kuma bunƙasa rayuwar jama’a.

Lawal

Gwamnan ya yi kira ga sarakuna, shugabannin al’umma, ‘yan kasuwa, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin kula da waɗannan ayyuka domin su ɗore su ci gaba da anfani ga jama’a na dogon lokaci.

 

Ya ce duk inda jama’a suka ji cewa su na da hannu a dukiyar jama’a, to za su fi bada kariya da kulawa, wanda hakan zai tabbatar da ɗorewar ci gaba a faɗin jihar.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.