ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
5 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar Tsafe, a wani bangare na shirinsa na farfaɗo da inganta muhimman cibiyoyin jama’a a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kona Ofishin ‘Yansanda, Coci Tare Da Garkuwa Da Waus A Neja
  • Karuwar Mace-mace A Asibitocinmu Sakamakon Sakacin Jami’an Lafiya

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sabunta tashar mota ta zamani, gyaran kasuwa, gyaran makaranta, sabuntawa da kuma samar da kayayyakin aiki a babban asibitin Tsafe, da kuma gyaran fadar sarkin Tsafe.

 

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

A cewar sanarwar, waɗannan ayyuka suna taka muhimmiyar rawa a rayuwar al’umma, musamman a bangarorin shugabanci, kiwon lafiya, ilimi, kasuwanci da zirga-zirga, tare da ƙara danƙon zumunci da jin cewa jama’a na da hannu a ci gaban yankinsu.

Lawal

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya ce sabunta fadar sarkin Tsafe alama ce ta girmama al’ada da kuma tabbatar da darajar masarautu a tsarin shugabanci na ƙasa. Ya ce sarakuna na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, warware rikice-rikice da kuma haɗa kan al’umma.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da masarautu a matsayin abokan hulɗa wajen sake gina Zamfara da dawo da martabar ta.

 

A bangaren ilimi da bunƙasa jarin ɗan Adam, ya bayyana cewa inganta Kwalejin Kiwon Lafiya ta Tsafe na nufin zuba jari ne a kan makomar ma’aikatan lafiya da za su yi hidima ga al’umma. A cewarsa, gyaran muhalli da kayan aikin makarantar zai ƙara inganta kwarewa da kwarin gwiwar ɗalibai.

 

Dangane da harkar lafiya kuwa, Gwamna Lawal ya ce sabunta babban asibitin Tsafe da samar masa da kayan aiki na zamani zai inganta ayyukan jinya, sauƙaƙa wa marasa lafiya da kuma taimaka wa ma’aikatan lafiya wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

 

Ya kuma jaddada cewa kasuwa da tashar mota na daga cikin ginshiƙan tattalin arzikin yankin, domin su ne ke haɗa manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da sauran jama’a. Sabunta waɗannan wurare, in ji shi, zai inganta tsari, tsaro da kuma bunƙasa rayuwar jama’a.

Lawal

Gwamnan ya yi kira ga sarakuna, shugabannin al’umma, ‘yan kasuwa, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin kula da waɗannan ayyuka domin su ɗore su ci gaba da anfani ga jama’a na dogon lokaci.

 

Ya ce duk inda jama’a suka ji cewa su na da hannu a dukiyar jama’a, to za su fi bada kariya da kulawa, wanda hakan zai tabbatar da ɗorewar ci gaba a faɗin jihar.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci
  • Sulaiman
    Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
  • Sulaiman
    Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara
  • Sulaiman
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.