ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
4 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar Tsafe, a wani bangare na shirinsa na farfaɗo da inganta muhimman cibiyoyin jama’a a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kona Ofishin ‘Yansanda, Coci Tare Da Garkuwa Da Waus A Neja
  • Karuwar Mace-mace A Asibitocinmu Sakamakon Sakacin Jami’an Lafiya

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sabunta tashar mota ta zamani, gyaran kasuwa, gyaran makaranta, sabuntawa da kuma samar da kayayyakin aiki a babban asibitin Tsafe, da kuma gyaran fadar sarkin Tsafe.

 

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

A cewar sanarwar, waɗannan ayyuka suna taka muhimmiyar rawa a rayuwar al’umma, musamman a bangarorin shugabanci, kiwon lafiya, ilimi, kasuwanci da zirga-zirga, tare da ƙara danƙon zumunci da jin cewa jama’a na da hannu a ci gaban yankinsu.

Lawal

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya ce sabunta fadar sarkin Tsafe alama ce ta girmama al’ada da kuma tabbatar da darajar masarautu a tsarin shugabanci na ƙasa. Ya ce sarakuna na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, warware rikice-rikice da kuma haɗa kan al’umma.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da masarautu a matsayin abokan hulɗa wajen sake gina Zamfara da dawo da martabar ta.

 

A bangaren ilimi da bunƙasa jarin ɗan Adam, ya bayyana cewa inganta Kwalejin Kiwon Lafiya ta Tsafe na nufin zuba jari ne a kan makomar ma’aikatan lafiya da za su yi hidima ga al’umma. A cewarsa, gyaran muhalli da kayan aikin makarantar zai ƙara inganta kwarewa da kwarin gwiwar ɗalibai.

 

Dangane da harkar lafiya kuwa, Gwamna Lawal ya ce sabunta babban asibitin Tsafe da samar masa da kayan aiki na zamani zai inganta ayyukan jinya, sauƙaƙa wa marasa lafiya da kuma taimaka wa ma’aikatan lafiya wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

 

Ya kuma jaddada cewa kasuwa da tashar mota na daga cikin ginshiƙan tattalin arzikin yankin, domin su ne ke haɗa manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da sauran jama’a. Sabunta waɗannan wurare, in ji shi, zai inganta tsari, tsaro da kuma bunƙasa rayuwar jama’a.

Lawal

Gwamnan ya yi kira ga sarakuna, shugabannin al’umma, ‘yan kasuwa, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin kula da waɗannan ayyuka domin su ɗore su ci gaba da anfani ga jama’a na dogon lokaci.

 

Ya ce duk inda jama’a suka ji cewa su na da hannu a dukiyar jama’a, to za su fi bada kariya da kulawa, wanda hakan zai tabbatar da ɗorewar ci gaba a faɗin jihar.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • Sulaiman
    ’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.