ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Manyan Ayyuka A Tsafe Domin Farfaɗo Da Ci Gaban Al’umma

by Sulaiman
6 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya sake jaddada cewa duk wani ci gaba da gwamnati za ta aiwatar dole ne ya kasance mai anfani kai tsaye ga rayuwar al’umma, tare da samar da sauyi mai ma’ana.

 

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin da ya ƙaddamar da muhimman ayyuka biyar a Ƙaramar Hukumar Tsafe, a wani bangare na shirinsa na farfaɗo da inganta muhimman cibiyoyin jama’a a faɗin jihar.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Bindiga Sun Kona Ofishin ‘Yansanda, Coci Tare Da Garkuwa Da Waus A Neja
  • Karuwar Mace-mace A Asibitocinmu Sakamakon Sakacin Jami’an Lafiya

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, an bayyana cewa ayyukan da aka ƙaddamar sun haɗa da sabunta tashar mota ta zamani, gyaran kasuwa, gyaran makaranta, sabuntawa da kuma samar da kayayyakin aiki a babban asibitin Tsafe, da kuma gyaran fadar sarkin Tsafe.

 

LABARAI MASU NASABA

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

A cewar sanarwar, waɗannan ayyuka suna taka muhimmiyar rawa a rayuwar al’umma, musamman a bangarorin shugabanci, kiwon lafiya, ilimi, kasuwanci da zirga-zirga, tare da ƙara danƙon zumunci da jin cewa jama’a na da hannu a ci gaban yankinsu.

Lawal

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Lawal ya ce sabunta fadar sarkin Tsafe alama ce ta girmama al’ada da kuma tabbatar da darajar masarautu a tsarin shugabanci na ƙasa. Ya ce sarakuna na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, warware rikice-rikice da kuma haɗa kan al’umma.

 

Gwamnan ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki kafaɗa da kafaɗa da masarautu a matsayin abokan hulɗa wajen sake gina Zamfara da dawo da martabar ta.

 

A bangaren ilimi da bunƙasa jarin ɗan Adam, ya bayyana cewa inganta Kwalejin Kiwon Lafiya ta Tsafe na nufin zuba jari ne a kan makomar ma’aikatan lafiya da za su yi hidima ga al’umma. A cewarsa, gyaran muhalli da kayan aikin makarantar zai ƙara inganta kwarewa da kwarin gwiwar ɗalibai.

 

Dangane da harkar lafiya kuwa, Gwamna Lawal ya ce sabunta babban asibitin Tsafe da samar masa da kayan aiki na zamani zai inganta ayyukan jinya, sauƙaƙa wa marasa lafiya da kuma taimaka wa ma’aikatan lafiya wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata.

 

Ya kuma jaddada cewa kasuwa da tashar mota na daga cikin ginshiƙan tattalin arzikin yankin, domin su ne ke haɗa manoma, ‘yan kasuwa, masu sana’o’i da sauran jama’a. Sabunta waɗannan wurare, in ji shi, zai inganta tsari, tsaro da kuma bunƙasa rayuwar jama’a.

Lawal

Gwamnan ya yi kira ga sarakuna, shugabannin al’umma, ‘yan kasuwa, ma’aikatan lafiya da masu ruwa da tsaki da su ɗauki alhakin kula da waɗannan ayyuka domin su ɗore su ci gaba da anfani ga jama’a na dogon lokaci.

 

Ya ce duk inda jama’a suka ji cewa su na da hannu a dukiyar jama’a, to za su fi bada kariya da kulawa, wanda hakan zai tabbatar da ɗorewar ci gaba a faɗin jihar.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba
  • Sulaiman
    Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu
  • Sulaiman
    Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

MASU ALAKA

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina
Labarai

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC
Manyan Labarai

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Next Post
Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

Binciken CGTN: Yadda Gwamnatin Tarayya Ke Gwabzawa Da Jihohi Ya Nuna Amurka Tana Yakar Kanta

LABARAI MASU NASABA

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

Kamfanonin Waje 4,800 Sun Kara Yawan Jarinsu A Sin Yayin Da Sashen Manyan Fasahohi Ya Samu Gagarumin Ci Gaba

July 23, 2026
Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

Sin Da Amurka Na Neman Ra’ayoyi A Kan Shirin Rage Haraji

July 23, 2026
Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

Binciken CGTN: Ya Kamata Kasashen Tekun Kudancin Sin Su Rike Ragamar Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankalin Yankin A Hannunsu

July 23, 2026
Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

Radda Ya Ƙaddamar Da Sabbin Ayyuka, Ya Kara Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa A Katsina

July 23, 2026
Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

Wadanne Dalilai Ne Suke Sabbaba Karin Karbuwar Sin Tsakanin Al’ummun Duniya?

July 23, 2026
Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

Ƙasashen Yankin Sahel 3 Sun Nuna Sha’awar Karɓar Bakuncin Gasar AFCON Ta 2032

July 23, 2026
Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

Sin Ta Kaddamar Da Shirin Shekaru Biyar Na Bunkasa Makamashi Da Ake Iya Sabuntawa  

July 23, 2026
Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

Wasikar Trump Ba Za Ta Taimaki Tinubu Ya Lashe Zaɓen 2027 Ba – ADC

July 23, 2026
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 25 Da Daddale Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Sada Zumunta A Tsakanin Sin Da Rasha

July 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio

July 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.