Memban hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyya kwaminis ta Sin, kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya gana da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio a jiya Laraba a birnin Manila na kasar Phillippines.
A yayin ganawar tasu, Wang Yi ya bayyana cewa, shekarar bana muhimmiyar shekara ce a fannin raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka. Shugabannin kasashen biyu sun yi ganawa a birnin Beijing cikin nasara, inda suka tabbatar da raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu bisa manyan tsare-tsare, da kuma gabatar da taswirar kokarin raya ta. Kazalika, Wang Yi ya gabatar da matsayin Sin dangane da jerin ra’ayoyi game da kasar Sin marasa dacewa, wadanda bangaren Amurka ya gabatar a kwanakin baya.
Ya kuma bukaci bangaren Amurka da ya girmama moriyar kasar Sin, da bin ka’idar kasancewar Sin daya tak a duniya, da daidaita matsalolin dake kasancewa a tsakaninsu, da warware batutuwan da Sin take dora muhimmanci kan su, don kare damar raya dangantakar dake tsakanin kasashen biyu yadda ya kamata.
A ganin bangarorin biyu, wannan ganawa tana da babbar ma’ana, sun kuma amince da aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito a kansu, da amfani da hanyar siyasa da diplomasiyya, da shirya mu’amalar manyan shugabannin kasashen biyu a nan gaba, don sa kaimi ga raya dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka bisa manyan tsare-tsare yadda ya kamata. (Zainab Zhang)














