Aƙalla manoma sama da 20 ne suka rasa rayukansu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari wasu ƙauyuka da ke Jihar Zamfara a ranar Laraba, kamar yadda ƙungiyar Amnesty International ta bayyana.
Rahotanni sun ce manoman na komawa daga gonakinsu ne lokacin da maharan suka kai musu hari.
Wani da ya tsallake rijiya da baya daga harin ya shaida wa BBC Hausa, cewa maharan sun zo ne da babura masu yawa, suka kewaye mutanen, sannan suka riƙa bin su suna harbewa.
Ya ce, duk wanda ya yi ƙoƙarin guduwa, ‘yan bindigar kan bi shi da babur, su harbe shi, sannan su tattake shi.
Haka kuma sun tattara dabbobin mutanen sannan suka tafi da su.
Majiyar ta ce maharan sun kai kimanin 100, kuma sun fito ne daga yankin Jangebe.
Ya ƙara da cewa ya ga gawarwakin mutane sama da 20 da idonsa.
An kai harin ne a ƙauyukan Sauna, Tudun Namale, Tsangaya, Mashekari da kuma Unguwar Shanu.
A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook, Amnesty International ta ce mutane 24 ne aka kashe, yayin da wasu da dama suka jikkata.
Ƙungiyar ta ce hare-haren na nuna cewa matakan da ake ɗauka wajen magance matsalar tsaro a Zamfara ba su samar da sakamakon da ake buƙata ba.
Amnesty ta kuma ce ‘yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare ƙauyukan jihar, inda a wasu lokuta suke sanar da mazauna ƙauyukan kafin su kai hari tare da neman haraji ko kuɗin fansa.
Jihar Zamfara da wasu jihohin Arewa maso Yamma na fama da hare-haren ‘yan bindiga sama da shekara 10, inda ake kashe mutane, sace su domin neman kuɗin fansa, tare da ƙone gidaje da lalata dukiyoyi.
Duk da cewa hukumomin tsaro na cewa suna ɗaukar matakan shawo kan matsalar, hare-haren na ci gaba da aukuwa a yankunan da abin ya shafa.













