ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 23, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

by Sadiq
46 minutes ago

Aƙalla manoma sama da 20 ne suka rasa rayukansu bayan da ‘yan bindiga suka kai hari wasu ƙauyuka da ke Jihar Zamfara a ranar Laraba, kamar yadda ƙungiyar Amnesty International ta bayyana.

Rahotanni sun ce manoman na komawa daga gonakinsu ne lokacin da maharan suka kai musu hari.

Wani da ya tsallake rijiya da baya daga harin ya shaida wa BBC Hausa, cewa maharan sun zo ne da babura masu yawa, suka kewaye mutanen, sannan suka riƙa bin su suna harbewa.

ADVERTISEMENT

Ya ce, duk wanda ya yi ƙoƙarin guduwa, ‘yan bindigar kan bi shi da babur, su harbe shi, sannan su tattake shi.

Haka kuma sun tattara dabbobin mutanen sannan suka tafi da su.

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

Majiyar ta ce maharan sun kai kimanin 100, kuma sun fito ne daga yankin Jangebe.

Ya ƙara da cewa ya ga gawarwakin mutane sama da 20 da idonsa.

An kai harin ne a ƙauyukan Sauna, Tudun Namale, Tsangaya, Mashekari da kuma Unguwar Shanu.

A wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook, Amnesty International ta ce mutane 24 ne aka kashe, yayin da wasu da dama suka jikkata.

Ƙungiyar ta ce hare-haren na nuna cewa matakan da ake ɗauka wajen magance matsalar tsaro a Zamfara ba su samar da sakamakon da ake buƙata ba.

Amnesty ta kuma ce ‘yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare ƙauyukan jihar, inda a wasu lokuta suke sanar da mazauna ƙauyukan kafin su kai hari tare da neman haraji ko kuɗin fansa.

Jihar Zamfara da wasu jihohin Arewa maso Yamma na fama da hare-haren ‘yan bindiga sama da shekara 10, inda ake kashe mutane, sace su domin neman kuɗin fansa, tare da ƙone gidaje da lalata dukiyoyi.

Duk da cewa hukumomin tsaro na cewa suna ɗaukar matakan shawo kan matsalar, hare-haren na ci gaba da aukuwa a yankunan da abin ya shafa.

MASU ALAKA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio
Manyan Labarai

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Hisbah
Manyan Labarai

Rajistar Shirin Auren Gata Na Kano Kyauta Ce, In Ji Hukumar Hisbah

July 22, 2026

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

‘Yan Bindiga Sun Hallaka Manoma Sama Da 20 A Zamfara – Amnesty International

July 23, 2026
Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

Sarkin Katagum Ya Jagoranci Addu’ar Roƙon Ruwa A Azare

July 23, 2026
Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

Me Ya Sa Ra’ayin Duniya Ke Karkata Zuwa Sin Yayin da Tasirin Amurka Ke Faduwa?

July 23, 2026
Cire Tallafi: Majalisar Nasarawa Za Ta Binciki Yadda Aka Karkatar Da Kayan Tallafin Jihar

Gwamnan Nasarawa Ya Sallami Kwamishinoni Shida Na Majalisar Zartarwar Jihar

July 23, 2026
Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP,  Sun Kashe ’Yan Ta’adda 20 A Yobe

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Amince Da Kafa Sabuwar Bataliyar Sojoji A Jihar Kwara

July 23, 2026
Akpabio

Tinubu Ya Dukufa Wajen Kawar Da Matsalar Tsaro — Akpabio

July 23, 2026
Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

Taron AI Na Duniya: Kaya Ya Kwance A Tushen Kaba

July 22, 2026
Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

Inganta Makarantu: Gwamna Lawal Ya Sanya Hannu Kan Dokokin Gyaran Ilimi A Zamfara

July 22, 2026
An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

An Kaddamar Da Taron Kasa Da Kasa Na Bunkasa Hanyar Siliki Ta Dijital Na 2026

July 22, 2026
Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

Amit Bhatia Na Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Sayen Kaso 30 Na Liverpool FC

July 22, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.