ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Haramta Karbar Kuɗaɗen Shiga Da Tsabar Kuɗi A Zamfara

by Sulaiman
3 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi a faɗin jihar, domin ƙarfafa tsarin fasahar zamani, haɗa bayanan hukumomi wuri guda, bai wa gwamnati damar sa ido kai tsaye, da kuma rage asarar kuɗaɗen shiga ta hanyar toshe duk wata kafa ta bayan fage.

 

Gwamnan ya bayyana wannan umarni ne a ranar Juma’ar da ta gabata yayin taron tattaunawa da wayar da kai kan Dokokin Gyaran Haraji na Nijeriya 2025, wanda Hukumar Tara Harajin Cikin Gida ta Jihar Zamfara ta shirya a Gusau, babban birnin jihar.

ADVERTISEMENT
  • Matatar Dangote Ta Ƙara Farashin Fetur, Ta Dakatar Da Lodi
  • Kotu Ta Ƙi Amincewa Da Bukatar Tsoffin Kwamishinonin Kano Na Riƙe Motocin Gwamnati

A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taron mai taken “Bunƙasa Hanyoyin Samun Kuɗaɗen Shiga a Sabon Tsarin Haraji: Binciko Damar Kuɗaɗen Shiga Da Ba Na Haraji Ba A Zamfara” ya tattaro dukkan masu ruwa da tsaki daga sassan jihar.

 

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Manufar taron ita ce samar da fahimta mai zurfi da haɗin kai yayin da jihar ke shirin aiwatar da sabon tsarin haraji.

 

A jawabinsa, Gwamna Lawal ya bayyana cewa Dokokin Gyaran Haraji na 2025 sun sake fasalin tsarin haraji a ƙasa baki ɗaya, inda aka fayyace iyakoki, aka daidaita hanyoyin aiki, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin matakan gwamnati uku.

 

Ya ce, rattaba hannu kan dokar sake fasalin Dokar Haɗaɗɗen Asusun Kuɗaɗen Shiga na Jihar Zamfara, wato Zamfara State Consolidated Revenue Law ya ƙara bai wa hukumar karbar kuɗaɗen shiga ta jihar ƙarfin ikon tantancewa, karba da kuma lissafa dukkan kuɗaɗen shiga na jihar, tare da daidaita kuɗaɗen haraji da waɗanda ba na haraji ba a ƙarƙashin tsari guda.

 

A cewarsa, gyare-gyaren sun zo da dama da kuma nauyi. Damar ita ce gina tsarin kuɗaɗen shiga na zamani, mai inganci da ke kare masu biyan haraji tare da ƙarfafa kwarin gwiwar masu zuba jari. Nauyin kuwa shi ne dukkan hukumomin gwamnati su daidaita aikinsu da sabon tsarin doka da gudanarwa.

 

Gwamnan ya jaddada cewa tara kuɗaɗen shiga ba aikin hukuma guda ba ne, illa wajibi ne na dukkan ma’aikatu, sassa da hukumomi. Duk wata hukuma da ke karbar kuɗi ta hanyar kuɗaɗe, lasisi, izini ko hidima dole ta tabbatar da gaskiya, daidaito da miƙa kuɗaɗe cikin gaggawa ta hanyoyin da aka amince da su.

 

Ya gargaɗi cewa duk wata hanya ta boye-boye, maimaituwa ko karbar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba za a ɗauki mataki a kai. Ya bayyana aniyar gwamnatinsa na rufe dukkan gibin da ke haddasa asarar kuɗaɗen shiga domin tabbatar da cewa kuɗaɗen da aka tara suna komawa wajen ci gaban jama’a.

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa alƙaluman IGR na 2025 sun nuna an samu ci gaba, amma har yanzu akwai buƙatar ƙara ƙarfafa tsarin tattara kuɗaɗen shiga. Ya ce burin jihar na tara tsakanin Naira biliyan 38 zuwa 42 ya ginu ne kan ajandar gyaran da aka fara da kuma faɗaɗa tsarin bin ƙa’ida.

 

A yayin taron, an karrama wasu ma’aikatu, hukumomi da ɗaiɗaikun mutane bisa jagoranci da ƙwazo wajen miƙa kuɗaɗen shiga ga gwamnati yadda ya kamata.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Sojoji Sun Kama Manyan Ƙunshin Tabar Wiwi 296 A Jihar Ogun

Sojoji Sun Kama Manyan Ƙunshin Tabar Wiwi 296 A Jihar Ogun

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.