ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jinjina Wa Dakarun Soji Bisa Nasarorin Da Suka Samu Kan ’Yan Bindiga A Zamfara

by Sulaiman
4 weeks ago
Lawal

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yaba wa dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Joint Task Force (North West) Operation Fansan Yamma bisa manyan nasarorin da suka samu a yaƙi da ’yan bindiga a sassan jihar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ranar 10 ga watan Mayun 2026, ya bayyana cewa dakarun rundunar sun kai wani gagarumin farmaki mai cike da tsari da haɗin kai a safiyar ranar Alhamis, 7 ga watan Mayu, 2026, a ƙananan hukumomin Kaura Namoda da Birnin Magaji na jihar Zamfara.Sanarwar ta ce, bayan artabun da aka yi da miyagun, jami’an tsaron sun kashe shugabannin ƙungiyoyin ‘yan bindiga uku tare da ƙwato tarin makamai da harsasai.

Kayayyakin da aka ƙwato sun haɗa da bindigar AK-47 guda ɗaya, bindigar mashin gon guda ɗaya, bindiga ƙirar gida guda ɗaya, gidan harsashin bindiga guda bakwai da kuma harsasai 571.

ADVERTISEMENT

Gwamna Dauda Lawal ya bayyana sabon farmakin da rundunar sojin ta ƙaddamar a matsayin abin yabawa kuma da ya zo a kan lokaci, musamman sakamakon nasarar da aka samu a ranar 10 ga watan Mayun 2026, inda aka tarwatsa wani babban taron shugabannin ‘yan ta’adda tare da kashe wasu manyan kwamandojinsu.

Rahotanni sun nuna cewa dakarun sun kai farmakin ne bayan samun bayanan sirri da suka tabbatar da cewa ‘yan ta’addar sun taru a wani buyayyen wuri da ke ƙauyen Tumfa a Ƙaramar Hukumar Shinkafi, domin tsara sabbin hare-hare da ayyukan ta’addanci kan al’ummomin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

Bangaren rundunar sojin sama ya kai wani ingantaccen harin sama kan maboyar ‘yan ta’addar, inda aka lalata ginin da suke amfani da shi a matsayin wurin taronsu.

Gwamna Lawal ya sake jaddada aniyar gwamnatin jihar Zamfara na ci gaba da bai wa rundunar soji da sauran hukumomin tsaro cikakken goyon baya da kayan aiki domin yaƙi da matsalar tsaro a jihar.

Lawal
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana
  • Sulaiman
    Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya
  • Sulaiman
    Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Sulaiman
    Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato
Labarai

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Next Post
Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Musayar Ra`ayoyi Kan Manyan Batutuwa

Shugabannin Sin Da Amurka Za Su Yi Musayar Ra`ayoyi Kan Manyan Batutuwa

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.