Shugaban hukumar kula da tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA Dakta Abubakar Dantsoho, ya sanar da goyon baya ga yarjejeniyar shirin bayar da horo a fannin bunkasa shuganabancin tafiyar da Tashoshin Jiragen Ruwa da ke a jihohin kasar da kuma a daukacin Afirka ta Yamma da ta Tsakiya.
A cewarsa, jarjejeniyar wacce aka kulla ta a Abuja, Dantsoho ya ce, hakan zai kara taiamaka wa, a fannin bunkasa fanin.
A jawabinsa a wajen kaddamar da shirin Dantsoho, ya kara nanata kudurin NPA, domin cimma burin shirin, musamman domin a samar da kariya a Tekuna da ingantaccen tsaro a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar da kuma a daukacin Afirka ta Yamma da ta Tsakiya.
Ya ce, an tsara bayar da horon ne, domin a kara ilimantarwa da samar da kayan aiki, da kwarewa, musamman wadanda ayyukansu, za su yi daidai da na fadin duniya.
Dantsoho ya yabawa Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Teku Adegboyega Oyetola, shugaban shirin na Abuja, Ministan kula da sufuri da kula da ayyuka na kasar Gambiya, kan kokarin da suke ci gaba da yi, na kara habaka fannin.
A cewarsa, zagewarsu, ta kara taimaka wa, wajen yin shugabanci na gari, tare da kuma burin cimma manufofofin yarjejeniyar.














