Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya yi bayani kan shirye-shiryen ziyarar aiki ta shugaban Amurka Donald Trump a kasar Sin daga ranar 13 zuwa 15 ga watan nan a gun taron manema labarai na yau da kullum.
Ya ce ganawar ta wannan karo za ta zama karo na farko da shugabannin kasashen biyu za su yi hira ta fuska da fuska tun bayan ganawar Busan a watan Oktoban shekarar bara, kuma ziyara ce ta farko da shugaban Amurka zai kawo kasar Sin cikin shekaru tara da suka gabata.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai yi musayar ra’ayoyi masu zurfi da shugaba Trump kan manyan batutuwa da suka shafi dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da kuma batutuwan da suka shafi zaman lafiya da ci gaban duniyaBugu da kari, Guo ya kuma bayyana cewa dangantakar diflomasiyya tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka ta taka muhimmiyar rawa ga kyautatuwar dangantakar kasashen biyu.
Kasar Sin tana son yin aiki tare da Amurka, wajen kiyaye ka’idojin daidaito, girmama juna, da kuma cin gajiyar juna don fadada hadin gwiwa, da warware sabani, da kuma kara samun kwanciyar hankali da tabbaci a cikin duniyar da ke cike da sauye-sauye.(Safiyah Ma)















Discussion about this post