Tsohon Shugaban Ƙasa, Goodluck Jonathan, ya musanta rahoton da ke zargin cewa an yi masa tayin Naira biliyan 500 ko kuma yana da hannu a wani shiri na raba ƙuri’un yankin Kudu Maso Kudu gabanin babban zaɓen shekarar 2027. Jonathan ya bayyana rahoton a matsayin na ƙarya marar tushe, tare da yin kira ga ’yan Nijeriya da su yi watsi da shi.
A cikin wata sanarwa da Mai Ba shi Shawara na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai, Dakta Ikechukwu Eze, ya fitar ranar Lahadi a Abuja, ya ce rahoton ƙagaggen labari ne da aka ƙirƙira domin yaudarar jama’a da kuma jefa tsohon shugaban ƙasar cikin cece-kuce na siyasa. Ya jaddada cewa Jonathan bai taɓa halartar wani taro ko shiga wata tattaunawa ko yarjejeniya da ta shafi wannan zargi ba.
Eze ya bayyana cewa tun bayan barin mulki a shekarar 2015, Jonathan ya ci gaba da kasancewa jagoran ƙasa mai mutunta dimokuraɗiyya, inda yake inganta zaman lafiya, shugabanci nagari da ingantaccen tsarin dimokuraɗiyyar a Nijeriya da sauran ƙasashen Afrika. Ya ƙara da cewa ƙoƙarin yaɗa irin waɗannan rahotanni na ƙarya na da nufin bata sunansa da kuma haifar da tashin hankali na siyasa ba tare da wani dalili ba.
Mai taimaka masa kan yaɗa labarai ya kuma yi kira ga kafafen yaɗa labarai da al’umma su riƙa tantance sahihancin rahotannin siyasa masu muhimmanci kafin wallafawa ko yaɗa su. Ya nanata cewa duk wata sanarwa ko matsaya daga tsohon shugaban ƙasar za a fitar da ita ne kawai ta hanyoyin sadarwa da aka amince da su, yana mai sake jaddada cewa Jonathan zai ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da zaman lafiya, haɗin kan ƙasa da ƙarfafa dimokuraɗiyya, ba tare da barin zarge-zargen da ba su da tushe su karkatar da hankalinsa ba.













