Ɗan takarar kujerar majalisar dokokin Jihar Kaduna a ƙarƙashin jam’iyyar ADC, daga mazaɓar Kawo, Honarabul Aminu Adam, ya bayyana cewa ƙarancin ilimin addini da rashin tarbiyya na daga cikin manyan abubuwan da ke jefa wasu matasa cikin aikata munanan laifuka, ciki har da kashe mutanen da ba su ji ba, ba su gani ba.
Honourable Aminu ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala taron saukar karatun alƙurani na makarantar Jodan da ke Kaduna, inda ya nuna damuwarsa kan yadda ake samun ƙaruwar matsalolin tsaro da kuma yadda wasu matasa ke ɗaukar doka a hannunsu ba tare da bin hanyoyin da doka ta tanada ba.
Ya ce, duk da cewa hukumomin tsaro na ci gaba da ƙoƙarin magance matsalar rashin tsaro, akwai buƙatar iyaye, malamai da shugabannin al’umma su taka rawar gani wajen tarbiyyantar da matasa tare da koya musu kyawawan ɗabi’u da darussan addini tun suna ƙanana.
A cewarsa, tarbiyya ita ce ginshiƙin zaman lafiya a kowace al’umma, kuma idan iyaye suka sauke nauyin da ya rataya a wuyansu na kula da tarbiyyar ƴaƴansu, za a rage yawan matasan da ke faɗawa cikin aikata laifuka da ɗaukar doka a hannu.
“Ya zama wajibi iyaye su sanya ido sosai kan halayen ƴaƴansu tare da tabbatar da suna samun ingantacciyar tarbiyya da ilimin addini. Idan aka yi haka, za a samu raguwar matsalolin da suka shafi tashin hankali da aikata laifuka,” in ji shi.
Honourable Aminu ya ƙara da cewa ilimin addini yana koya wa mutum sanin darajar rayuwa, haƙurin zaman tare da mutunta doka, yana mai cewa duk matashin da aka gina bisa kyakkyawar tarbiyya ba zai kasance cikin masu aikata kisan gilla ko sauran miyagun ayyuka ba.
Ya yi kira ga gwamnati, malamai, ƙungiyoyin addini da na farar hula da su haɗa kai wajen wayar da kan matasa kan illolin tashin hankali, shaye-shaye da ɗaukar doka a hannu, domin samar da al’umma mai cike da zaman lafiya da haɗin kai.
Ɗan takarar ya jaddada cewa magance matsalar rashin tsaro aiki ne da ya rataya a wuyan kowa da kowa. Ya ce idan iyaye suka ba da muhimmanci ga tarbiyya da ilimin addini, al’umma za ta samu matasa nagari masu mutunta rayuwa da bin doka.














