ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

by Abubakar Sulaiman
1 hour ago

Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai da kisan wasu ‘yan Nijeriya biyu a Afrika ta Kudu, tare da buƙatar hukumomin ƙasar su gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa domin kamowa tare da hukunta waɗanda ke da hannu a lamarin. Haka kuma, gwamnatin ta nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan Nijeriya da sauran baƙi da ke zaune a ƙasar.

A cikin wata sanarwa da kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya fitar, an bayyana mamatan da sunan Emeka Charles Iroegbu da Musa Yunana Joe, wanda aka fi sani da Big Joe. Sanarwar ta ce ana zargin jami’an ‘yansandan Tshwane Metro ne suka kashe Iroegbu a ranar 28 ga Yuni, 2026, a Sunnyside da ke Pretoria yayin wani bincike, yayin da Big Joe kuma wasu da ba a tantance ba suka harbe shi a gaban shagonsa da ke Witbank a lardin Mpumalanga.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta ce jami’an da ake zargi da kashe Iroegbu su ne kuma ake zargi da kashe wani ɗan Nijeriya, Nnaemeka Mathew Andrew Ekpenyong, a ranar 20 ga Afrilu, 2026, duk da cewa har yanzu ba a kama su ba. Ta kuma yi tir da kalaman wani jami’in gwamnatin Afrika ta Kudu da ya danganta ‘yan Nijeriya da safarar miyagun ƙwayoyi, tana mai cewa irin waɗannan kalamai na ƙarfafa ƙiyayya da hare-hare kan baƙi.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu su kasance masu bin doka tare da gujewa wuraren da ke da haɗarin tashin hankali, yayin da ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya da kuma fitar da ‘yan Nijeriya da suka yi rajista daga ƙasar.

Ta kuma jaddada cewa Afirka ta Kudu na da alhakin kare rayuka da dukiyoyin baƙi, tare da gargaɗin cewa idan hare-haren suka ci gaba, Nijeriya za ta yi la’akari da ɗaukar wasu matakai.

LABARAI MASU NASABA

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana
  • Abubakar Sulaiman
    Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC
  • Abubakar Sulaiman
    Mutane 600 Ne Kacal Suka Ci Jarabawar Ɗaukar Malaman Firamare Daga Cikin 8,000

MASU ALAKA

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano
Labarai

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Next Post
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026
Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

Nasiha Ga Uwargida Kan Zafin Kishi (2)

July 5, 2026
Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Musaya Da Sweden A Dukkanin Fannoni

July 5, 2026
Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

Messi Da Mbappé Na Jagorantar Cin Ƙwallaye A Gasar Kofin Duniya

July 5, 2026
Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Kafa Cibiyar NIPHID: NCDC Ta Yi Kuskuren Fahimtar Ƙudirin Dokar

July 5, 2026
Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

Dalilan Da Suka Jawo Aka Ƙi Yin Maraba Da FIM House A Jihar Kano

July 5, 2026
Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.