Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai da kisan wasu ‘yan Nijeriya biyu a Afrika ta Kudu, tare da buƙatar hukumomin ƙasar su gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa domin kamowa tare da hukunta waɗanda ke da hannu a lamarin. Haka kuma, gwamnatin ta nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan Nijeriya da sauran baƙi da ke zaune a ƙasar.
A cikin wata sanarwa da kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya fitar, an bayyana mamatan da sunan Emeka Charles Iroegbu da Musa Yunana Joe, wanda aka fi sani da Big Joe. Sanarwar ta ce ana zargin jami’an ‘yansandan Tshwane Metro ne suka kashe Iroegbu a ranar 28 ga Yuni, 2026, a Sunnyside da ke Pretoria yayin wani bincike, yayin da Big Joe kuma wasu da ba a tantance ba suka harbe shi a gaban shagonsa da ke Witbank a lardin Mpumalanga.
Bugu da ƙari, gwamnatin ta ce jami’an da ake zargi da kashe Iroegbu su ne kuma ake zargi da kashe wani ɗan Nijeriya, Nnaemeka Mathew Andrew Ekpenyong, a ranar 20 ga Afrilu, 2026, duk da cewa har yanzu ba a kama su ba. Ta kuma yi tir da kalaman wani jami’in gwamnatin Afrika ta Kudu da ya danganta ‘yan Nijeriya da safarar miyagun ƙwayoyi, tana mai cewa irin waɗannan kalamai na ƙarfafa ƙiyayya da hare-hare kan baƙi.
Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu su kasance masu bin doka tare da gujewa wuraren da ke da haɗarin tashin hankali, yayin da ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya da kuma fitar da ‘yan Nijeriya da suka yi rajista daga ƙasar.
Ta kuma jaddada cewa Afirka ta Kudu na da alhakin kare rayuka da dukiyoyin baƙi, tare da gargaɗin cewa idan hare-haren suka ci gaba, Nijeriya za ta yi la’akari da ɗaukar wasu matakai.














