ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

by Abubakar Sulaiman
3 weeks ago

Gwamnatin Tarayya ta yi Allah-wadai da kisan wasu ‘yan Nijeriya biyu a Afrika ta Kudu, tare da buƙatar hukumomin ƙasar su gudanar da cikakken bincike cikin gaggawa domin kamowa tare da hukunta waɗanda ke da hannu a lamarin. Haka kuma, gwamnatin ta nuna damuwa kan abin da ta bayyana a matsayin ci gaba da kai hare-hare kan ‘yan Nijeriya da sauran baƙi da ke zaune a ƙasar.

A cikin wata sanarwa da kakakin Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya fitar, an bayyana mamatan da sunan Emeka Charles Iroegbu da Musa Yunana Joe, wanda aka fi sani da Big Joe. Sanarwar ta ce ana zargin jami’an ‘yansandan Tshwane Metro ne suka kashe Iroegbu a ranar 28 ga Yuni, 2026, a Sunnyside da ke Pretoria yayin wani bincike, yayin da Big Joe kuma wasu da ba a tantance ba suka harbe shi a gaban shagonsa da ke Witbank a lardin Mpumalanga.

Bugu da ƙari, gwamnatin ta ce jami’an da ake zargi da kashe Iroegbu su ne kuma ake zargi da kashe wani ɗan Nijeriya, Nnaemeka Mathew Andrew Ekpenyong, a ranar 20 ga Afrilu, 2026, duk da cewa har yanzu ba a kama su ba. Ta kuma yi tir da kalaman wani jami’in gwamnatin Afrika ta Kudu da ya danganta ‘yan Nijeriya da safarar miyagun ƙwayoyi, tana mai cewa irin waɗannan kalamai na ƙarfafa ƙiyayya da hare-hare kan baƙi.

ADVERTISEMENT

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ‘yan Nijeriya da ke Afirka ta Kudu su kasance masu bin doka tare da gujewa wuraren da ke da haɗarin tashin hankali, yayin da ta ce tana ci gaba da ƙoƙarin diflomasiyya da kuma fitar da ‘yan Nijeriya da suka yi rajista daga ƙasar.

Ta kuma jaddada cewa Afirka ta Kudu na da alhakin kare rayuka da dukiyoyin baƙi, tare da gargaɗin cewa idan hare-haren suka ci gaba, Nijeriya za ta yi la’akari da ɗaukar wasu matakai.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.