A wannna makon, za mu saurari ra’ayoyin masu karatunmu ne a kan shirin ƙirƙirro da ƴansanda jihohi da gwamnati ke shirin yi, wanda har majalisun ƙasa sun zartar da ƙudurin dokar, shin kuna ganin hakan zai kai ga kawo ƙarshen matsalolin tsaron da ake fuskanta a sassan ƙasar nan? Ga dai bayanan da muka samu, kamar yadda Sani Anwar ya tattara mana.
Umar Hussain Zam-zam, daga Jihar Kaduna
Mai fashin baƙi a kan harkokin yau da kullum a Jihar Kaduna, ya ce, “Samar da Ƴansandan jihohi, ba shi da wani alfanu a halin da muke ciki a ƙasar nan, dalili kuwa shi ne, kawai dai za a bai wa ƴan siyasa damar yin abin da suke so ne. Kar a manta fa, kwamishinan ƴansanda ba ya karɓar amsar umarni daga Sufeto Janar na ƴansandan Nijeriya, amma ka ga duk da haka ana samun matsala, ina kuma a ce sun koma ƙarƙashin gwamnonin jihohi.
Sunana Honarabul Sadiƙ Umar Ashafa, daga Jihar Kaduna
Ɗan siyasa, kuma masanin harkokin tsaro a Jihar Kaduna, ya ce; samar da ƴansandan jihohi, akwai alfanu ta wata fuskar, kuma akwai tangarɗa a ɗaya fuskar. “Da farko dai, tsaro shi ne rayuwar Ɗan’adam, musamman ma talaka, wanda yanzu an samu matsala a kai.
Samar da ƴansandan jihohi, zai taimaka wajen rage yawaitar ta’addanci, saboda zai taimaka wa jihohi wajen ganin an rage samun yawaitar matsalar tsaro.
“A Wani ɓangaren kuma, akwai yiwuwar gwamonin jihohi, za su riƙa amfani da ƴansanda, wajen yin abin da suke so, wanda kuma hakan bai kamata ba. Dama gwamnanoni suna ganin cewa; ba sa iya juya ƴansanda, waɗanda suke ƙarƙashin gwamnatin tarayya, ka ga yanzu idan aka samu ƴansandan jihohi, gwamnoni za su yi abin da suke so.
Sunana Usman Sani Amar, daga Abuja FCT
Tsaro na daga cikin manyan ginshiƙan ci gaban kowace ƙasa. A duk lokacin da rashin tsaro ya ƙaru, rayuwar al’umma da tattalin arziƙi sukan fuskanci barazana. Wannan ne ya sa batun kafa ƴansandan jihohi ya ci gaba da ɗaukar hankalin ƴan Nijeriya.
A ra’ayina, lokaci ya yi da ya kamata a yi nazari mai zurfi, kan kafa ƴansandan jihohi. Nijeriya ƙasa ce mai faɗin gaske, kuma yana da wuya rundunar ƴansandan tarayya kaɗai ta iya kula da harkokin tsaro yadda ya kamata a dukkan jihohin ƙasar.
Idan aka kafa ƴansandan jihohi, za su fi sanin al’adun yankunansu, yanayin muhalli da kuma mutanen da suke zaune a cikinsu. Wannan na iya taimakawa wajen gano masu aikata laifuka cikin sauri, tare da inganta tattara bayanan sirri da hana aikata laifi, tun kafin ya faru.
Sai dai kuma, akwai damuwar da ba za a yi watsi da ita ba. Wasu na tsoron cewa, gwamnonin jihohi na iya amfani da rundunar wajen cin zarafin masu adawa da su ko kuma nuna son kai wajen aiwatar da doka. Idan har ba a samar da ingantattun ƙa’idoji da tsarin sa ido mai zaman kansa ba, hakan na iya haifar da sabbin matsaloli, maimakon warware waɗanda ake fuskanta.
Sunana Bilkisu Maharazu, daga Jihar Katsina
Kafa ƴansandan jihohi, na iya taimakawa wajen magance rashin tsaro. Abu na farko da nake son magana a kai shi ne, matsalar rashin tsaro da ta daɗe tana addabar ƙasarmu. Wannan matsala, ta yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi, tare da jefa al’umma cikin fargaba da rashin kwanciyar hankali.
A ra’ayina, kafa ƴansandan jihohi na da matuƙar muhimmanci, idan har za a aiwatar da shi yadda ya kamata. Idan aka samar wa jami’an tsaro kayan aiki na zamani, aka ba su cikakken horo, aka biya su albashi mai kyau tare da inganta walwalarsu, kuma suka gudanar da aikinsu cikin gaskiya ba tare da cin hanci ko nuna son kai ba, ina da yaƙinin cewa; za a samu gagarumin ci gaba, wajen magance matsalar rashin tsaro.
Sunana Muhammad Idris Aliyu, CEO na Kamfanin
Sarkin Furniture International
A zahirin gaskiya, kuma a ra’ayina, ba na goyon bayan lamarin ƴansadan jiha da gwamnati ke son ta ƙirƙiro, sakamakon su kansu waɗanda gwamnatin tarayya ta ɗauka, ba a biyansu buƙatunsu kamar yadda ya dace, ballantana a ce yanzu ma ƴansanda jihohi, ta ina za su fara?
Ƴansanda abin girmamawa ne, sai dai kuma rashin kyakkyawan tsari a nan matsalar take, waɗanda ke ƙarƙashin gwamnatin tarayya, babu wani tsari mai kyau da suke fuskanta, su ma da suka daɗe cikin yanayin kenan, to ina kuma ga waɗanda ba a ma ɗauke su ba, ballantana a fara ganin kamun ludayinsu, ko da ma an ƙirƙire su, daga ina ne za su fara? aikin fa ya yi wa Kurege yawa.
Sunana Muhammad Nura wanda aka fi sani da Daddy
A zahirin gaskiya, a ra’ayina ina goyon bayan ƴansandan jiha da majalisar dattawa ta amince da a ƙirƙiro da su, sakamkon yawan da aka yi har ayyukan tsaro sun yi wa waɗanda ke ƙarƙashin gwamnatin tarayya yawa. Idan jihohi suna da nasu, kamar wani taimako ne suka yi wa gwamnatin tarayyar.
Bissalam, Allah ya ba mu zaman lafiya.
Sunana Umar Abdullahi, daga Jihar Zamfara
Kafa ƴansandan jihohi na da amfani wajen inganta tsaro, idan aka tsara su da dokoki masu ƙarfi, musamman a wuraren Sakkwato, Kebbi, Katsina da ma Zamfara, inda muke fuskantar matsalar tsaro. Babu shakka, za su taimaka wa ƴansandan tarayya wajen kula da tsaro da kuma sanin yankin da al’adun mutanen jihar. Amma illolinta kuma su ne, gwamnoni na iya amfani da su wajen tsoratar da abokan adawa na siyasa da kuma cin zarafin haƙƙin Ɗan’adam, idan ba a sanya ingantattun dokoki ba.














