Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta ƙaddamar da wani kwamiti na musamman kan Kuɗaɗen Tallafi (Endowment Fund Committee) domin tabbatar da gaskiya da riƙon amana, bunƙasa ilimi, da kuma samar da hanyoyin dogaro da kai na zamantakewa da tattalin arziki a faɗin Arewacin Nijeriya.
Tsohon Babban Sufeton Ƴansandan Nijeriya, Mohammed Dikko Abubakar (MD Abubakar) ne ke jagorantar wannan kwamiti, inda ake sa ran zai samar da ingantaccen jagoranci na fuskantar nasara da kuma sanya ido kan aiwatar da manufofin gajiyar da asusun.
Yayin da yake jawabi a gurin ƙaddamarwar ranar Talata, Shugaban ƙungiyar ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya bayyana cewa kafa wannan kwamiti wani gagarumin mataki ne na faɗaɗa damar samun ilimi, tallafa wa ci gaban al’umma, da kuma inganta ɗorewar ci gaba a yankin Arewa.
Dalhatu ya bayyana cewa asusun tallafin zai zama dandamali na magance manyan ƙalubalen ci gaba da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.
Ya bayyana cewa ƙungiyar ta taɓa ƙaddamar da Asusun Tallafi na Naira Biliyan 100
yayin bikin cikar ta shekaru 25 (Silɓer Jubilee), inda ya lura cewa duk da cewa masu taimako sun yi alƙawarin bayar da Naira Biliyan 7.8, Naira Biliyan 3.9 kacal aka iya karɓa zuwa yanzu.
A cewarsa, kuɗaɗen da aka karɓo ɗin suna nan ajiye cikin amana a wani asusun banki da ke (Jaiz Bank).
“Kuɗin suna nan lafiya ƙalau, kuma muna sa ran kwamitin ba wai kawai zai ƙaddamar da shirye-shiryen ayyukan jinƙai masu amfani a faɗin Arewa ba, har ma zai ƙarfafa gwiwar waɗanda suka yi alƙawuran baya domin su cika su. Kyawawan ayyukan da za mu yi da kuɗaɗen da muke da su a halin yanzu tabbas za su janyo hankalin mutane su ƙara ba mu wasu kuɗaɗen,” in ji shi.
Ayyukan da ke gaban kwamitin
Ana sa ran sabon Asusun Tallafin zai tara kayan aiki da kuɗaɗe domin: Shirye-shiryen bunƙasa ilimi. Tallafa wa matasa. Koyar da dabarun jagoranci.
Sauran ayyukan da ke da nufin inganta rayuwa da walwalar al’ummomi a faɗin Arewacin Nijeriya baki ɗaya.














