ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

by Rabi'u Ali Indabawa
1 hour ago
ACF

Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF) ta ƙaddamar da wani kwamiti na musamman kan Kuɗaɗen Tallafi (Endowment Fund Committee) domin tabbatar da gaskiya da riƙon amana, bunƙasa ilimi, da kuma samar da hanyoyin dogaro da kai na zamantakewa da tattalin arziki a faɗin Arewacin Nijeriya.

Tsohon Babban Sufeton Ƴansandan Nijeriya, Mohammed Dikko Abubakar (MD Abubakar) ne ke jagorantar wannan kwamiti, inda ake sa ran zai samar da ingantaccen jagoranci na fuskantar nasara da kuma sanya ido kan aiwatar da manufofin gajiyar da asusun.

Yayin da yake jawabi a gurin ƙaddamarwar ranar Talata, Shugaban ƙungiyar ACF, Alhaji Bashir Dalhatu, ya bayyana cewa kafa wannan kwamiti wani gagarumin mataki ne na faɗaɗa damar samun ilimi, tallafa wa ci gaban al’umma, da kuma inganta ɗorewar ci gaba a yankin Arewa.

ADVERTISEMENT

Dalhatu ya bayyana cewa asusun tallafin zai zama dandamali na magance manyan ƙalubalen ci gaba da ke fuskantar Arewacin Nijeriya.

Ya bayyana cewa ƙungiyar ta taɓa ƙaddamar da Asusun Tallafi na Naira Biliyan 100

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

yayin bikin cikar ta shekaru 25 (Silɓer Jubilee), inda ya lura cewa duk da cewa masu taimako sun yi alƙawarin bayar da Naira Biliyan 7.8, Naira Biliyan 3.9 kacal aka iya karɓa zuwa yanzu.

A cewarsa, kuɗaɗen da aka karɓo ɗin suna nan ajiye cikin amana a wani asusun banki da ke (Jaiz Bank).

“Kuɗin suna nan lafiya ƙalau, kuma muna sa ran kwamitin ba wai kawai zai ƙaddamar da shirye-shiryen ayyukan jinƙai masu amfani a faɗin Arewa ba, har ma zai ƙarfafa gwiwar waɗanda suka yi alƙawuran baya domin su cika su. Kyawawan ayyukan da za mu yi da kuɗaɗen da muke da su a halin yanzu tabbas za su janyo hankalin mutane su ƙara ba mu wasu kuɗaɗen,” in ji shi.

Ayyukan da ke gaban kwamitin

Ana sa ran sabon Asusun Tallafin zai tara kayan aiki da kuɗaɗe domin: Shirye-shiryen bunƙasa ilimi. Tallafa wa matasa. Koyar da dabarun jagoranci.

Sauran ayyukan da ke da nufin inganta rayuwa da walwalar al’ummomi a faɗin Arewacin Nijeriya baki ɗaya.

ACF
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

MASU ALAKA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci
Labarai

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda
Labarai

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara
Labarai

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Next Post
Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

Birtaniya Da Nijeriya Sun Ƙulla Yarjejeniya Kan Yaƙi Da Ta’addanci

June 26, 2026
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

ACF Ta Ƙaddamar Da Gidauniyar Tallafa Wa Ilimi A Arewa

June 26, 2026
Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

Damunar Bana: Yadda Gwamnati Da Manoma Ke Tunkarar Barazanar Ƴan Ta’adda

June 26, 2026
Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

Sin Da Amurka Sun Amince Da Kafa Majalisar Kasuwanci

June 25, 2026
Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

Mukaddashiyar Shugaban Venezuela Ta Yi Godiya Da Aniyar Sin Ta Ba Su Agaji

June 25, 2026
Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

Shugabar Namibia Ta Kaddamar Da Dakin Baje Kolin Kimiyya Da Sinawa Suka Gina

June 25, 2026
Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

Gwamna Lawal Ya Yi Alƙawarin Bayar Da Ƙarin Tallafi Ga Jami’an Tsaro A Zamfara

June 25, 2026
Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

Salon Jagorancin Kasar Sin Na Ingiza Samar Da Ci Gaba Mai Nagarta

June 25, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Dangote Ya Rage Farashin Fetur Zuwa N1,125 Kan Kowace Lita

June 25, 2026
Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

Adadin Injunan Samar Da Wutar Lantarki Da Sin Ya Wuce Kilowatts Awa Biliyan 4, Wato Ya Kai Ga Matsayi Na Farko A Duniya

June 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.