Shugaban hukumar ba da taimakon fasaha da kwararru ta Najeriya NTAC General Yusuf Buba Yakub, ya bayyana cewa, Najeriya na daukar darasi daga kyakkwar alakar diflomasiyya da jan hankali da kasar Sin ke amfani da shi, a kokarin da kasar ke yi na karfafa tasirinta a duniya, da karfafa hadin gwiwar kasashe masu tasowa, ta hanyar aikewa da taimakon kwararun ma’aikata zuwa kasashe.
Yakubu ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai a Abuja, babban birnin kasar, inda ya ba da misali da salon da Sin ke amfani da shi na hulda da kasashen waje, domin gina doguwar alaka ta hanyar hadin gwiwa.
Tun bayan kirkirar hukumar NTAC a shekarar 1987, ta tura ’yan Najeriya kwararru ’yan sa-kai sama da 10,000 zuwa kasashe sama da 40 a daukacin nahiyar Africa da yankin Caribbean da tsibiran Pacific, inda kwararrun suka bayar da gudummawa a fannoni da dama, da suka hada da fannin ilmi, magunguna, shari’a, injiniya, noma da kuma fasaha. (Mai Fassara: Suleiman Suleiman)














