Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu ya rage farashin man fetur tare da ɗaukar matakan rage tsadar rayuwa da ke ƙara jefa ’yan Nijeriya cikin wahala.
Atiku ya yi wannan kiran ne ranar Juma’a a Abuja, yayin da yake magana kan farashin man fetur, tallafin gwamnati da matsalolin tattalin arziƙin da ’yan Nijeriya ke fuskanta.
Ya ce cire tallafin man fetur ya ƙara tsadar sufuri, abinci, noma da harkokin kasuwanci, lamarin da ya ƙara wa iyalai da ma’aikata nauyi.
A cewar Atiku, ya kamata gwamnati ta sake duba manufofin da suka ƙara tsadar rayuwa, maimakon dogaro da rabon tallafi kawai.
Ya kuma yi gargaɗin cewa shirin cire tallafin wutar lantarki daga shekarar 2027 na iya ƙara jefa magidanta da ’yan kasuwa cikin ƙarin matsala, idan ba a yi la’akari da darusan da aka koya daga cire tallafin man fetur ba.
Atiku ya ce a shirye yake ya bai wa gwamnatin Tinubu shawarwari kan yadda za a rage farashin man fetur, ko da gwamnati za ta kalli shawarwarin da wani abu na daban.
Ya kuma bayyana tsarin da yake son amfani da shi kan man fetur gabanin zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Ya ce idan aka zaɓe shi, zai samar da tsarin tallafin man fetur na gaskiya a a kan man da aka tace a Nijeriya kuma aka sayar wa ’yan ƙasa.
Atiku ya ce tsarin zai kasance da iyakar kuɗin da za a kashe, sannan ya buƙaci amincewar Majalisar Dokoki ta Ƙasa da kuma gudanar da bincike mai zaman kansa.
Ya ce manufar shirin ita ce ƙarfafa tace man fetur a cikin gida tare da rage farashin mai ga masu amfani.














