A yau Juma’a 18 ga wata, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya jagoranci taron manema labarai da aka saba gudanarwa, inda aka tambaye shi, game da ganawar shugabannin kasashen Sin da Amurka.
Da yake ba da amsa game da tambayar, Guo Jiakun ya ce bangarorin biyu na Sin da Amurka suna ci gaba da tuntubar juna game da shirye-shiryen ganawar shugabannin biyu cikin shekarar nan. (Suleiman Suleiman)
ADVERTISEMENT














