Wani matashi da ya tsira daga inda sama da matasa 30 da suka rasu waɗanda ake zargi da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a Jihar Neja, ya yi zargin cewa an fesa wani sinadari a ɗakin da aka tsare su, kafin wasu daga cikinsu su fara faɗuwa.
Matashin da ya tsira ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a, yayin ziyarar da Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya kai jihar.
Ziyarar ta biyo bayan mutuwar mutane 33 da ake zargi da haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba, waɗanda ke hannun Hukumar Tsaron ta NSCDC.
A cewar matashin, an fesa wani abu a cikin ɗakin jim kaɗan shigar da su, sannan wasu daga cikinsu suka fara faɗuwa.
An kama waɗanda ake zargin ne yayin wani samame da aka gudanar kan haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba a yankin Wushishi/Lukoto na Jihar Neja a ranakun 15 da 16 ga watan Satumba.
Har yanzu ba a tabbatar da ainihin abin da ya yi sanadin mutuwar matasan ba, yayin da jami’an tsaro ke ci gaba da bincike.
Tun da farko, Ministan Harkokin Cikin Gida ya dakatar da Kwamandan NSCDC na Jihar Neja, Suberu Aniviye, tare da ba da umarnin gudanar da bincike kan lamarin.
Hukumar NSCDC ma ta kafa kwamitin bincike domin duba halin da waɗanda aka tsare suke ciki lokacin da aka kama su, yadda aka kula da su yayin da suke tsare.
Ana sa ran binciken zai gano abin da ya faru kafin mutuwar matasan.













