Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Nijeriya (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Kaduna (KASU), ta dakatar da yajin aikin da ta ke yi, bayan gwamnatin jihar ta amince da aiwatar da yarjejeniyar 2025 tsakanin Gwamnatin Tarayya da ƙungiyar.
ASUU da KASU sun sanar da dakatar da yajin aikin ne bayan taron majalisar ƙungiyar da aka gudanar ranar Alhamis, 17 ga watan Satumba 2026.
Ƙungiyar ta ce dakatarwar ta fara aiki da misalin ƙarfe 12:01 na safiyar ranar Juma’a, 18 ga watan Satumba.
Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya amince da fara aiwatar da yarjejeniyar daga albashin watan Oktoban 2026.
Haka kuma, Majalisar Gudanarwa da Hukumar Kula da Jami’ar sun amince da fara biyan malaman jami’ar bashin albashi na tsawon watanni tara da suke bi, daga watan Janairu zuwa Satumban 2026.
ASUU ta ce ta amince da matakan da gwamnati da jami’ar suka ɗauka, tare da bayyana cewa za ta shirya domin ci gaba da koyar da ɗalibai.
An fara yajin aikin ne saboda wasu buƙatun da suka shafi albashi, alawus-alawus da sauran sharuɗan aikin malaman jami’ar.
Don haka, dakatar da yajin aikin zai sa al’amuran harkokin karatu a Jami’ar Jihar Kaduna su ci gaba da gudana.













