Gwamnatin Tarayya ta dakatar da shirin sake duba kuɗin rajistar jarabawar kammala Sakandire ta WAEC da NECO na shekarar 2027, har sai an kammala tattaunawa da masu ruwa da tsaki.
A cikin wata sanarwa da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta fitar ranar Litinin, ta ce an janye sanarwar da ke ɗauke da shawarar ƙarin kuɗin rajistar, wadda aka rubuta ranar 18 ga Yunin 2026, domin ba da damar yin cikakken nazari da kuma tattaunawa da dukkan masu ruwa da tsaki kafin a yanke hukunci na ƙarshe.
Sanarwar, wadda Daraktar Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ta ma’aikatar, Boriowo Folasade, ta sanya wa hannu, ta bayyana cewa an dakatar da shirin ne bayan nuna damuwa da suka da jama’a suka bayyana.













