Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya soki shirin Gwamnatin Tarayya na ƙara kuɗin rajistar jarabawar WAEC da NECO zuwa Naira 50,000 daga shekarar 2027, yana mai bayyana matakin a matsayin wanda zai ƙara wa talakawa shan wahala.
A cikin wata sanarwa da mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar ranar Lahadi, Atiku ya ce ƙarin kuɗin zai sa ilimi ya ƙara zama mai wahalar samu ga yaran da suka fito daga gida mai ƙaramin ƙarfi, musamman a daidai lokacin da ‘yan Nijeriya ke fama da tsadar rayuwa. Ya jaddada cewa ilimi haƙƙi ne na kowane ɗan ƙasa, ba gata ba ne da masu kuɗi kaɗai za su iya samu.
Atiku ya yi gargaɗin cewa ƙarin kuɗin jarabawar na iya ƙara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya. A cewarsa, maimakon gwamnati ta ƙara wa iyaye nauyi, ya kamata ta samar da hanyoyin da za su sauƙaƙa samun ilimi tare da faɗaɗa damar shiga makarantu ga kowa.
Ya kuma yi nuni da cewa hana yara damar ci gaba da karatu saboda tsadar kuɗin jarabawa na iya jefa su cikin talauci, da rashin aikin yi da aikata laifuffuka. A kwanakin baya ne Gwamnatin Tarayya ta amince da sanya Naira 50,000 a matsayin kuɗin rajistar jarabawar WAEC da NECO ga ɗalibai daga shekarar karatu ta 2027, maimakon kusan Naira 27,500 da ake biya a halin yanzu.













