Aƙalla mutane tara daga iyali guda, ciki har da jariri mai wata biyu, suka rasa rayukansu bayan wasu mahara sun kai hari kan ƙauyukan Kum da Wereng-Camp da ke Ƙaramar Hukumar Riyom a Jihar Filato.
Rahotanni sun ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na daren Asabar, inda ya ɗauki sama da awa guda ana kai farmaki, yayin da shugaban ƙauyen ya samu munanan raunuka.Wani mazaunin yankin, Precious Tok, ya shaida cewa maharan sun afka wa al’ummar ƙauyukan, suna harbe-harbe, lamarin da ya tilasta wa mazauna tserewa zuwa cikin dazuka domin tsira da rayukansu.
Ya ce an kashe mutanen tara ne ƴan gida ɗaya a gidansu yayin harin, wanda ya bayyana a matsayin ɗaya daga cikin mafi muni da yankin ya fuskanta a baya-bayan nan.
Sakataren Yaɗa Labarai na Berom Youth Moulders Association, Rwang Tengwong, ya tabbatar da harin, yana mai cewa maharan sun yi amfani da duhun dare wajen kai farmakin kan fararen hula. Ya ce shugaban ƙauyen ya samu raunuka masu tsanani kuma an garzaya da shi asibiti domin samun kulawar likitoci. Ya ƙara da cewa an sanar da hukumomin tsaro, tare da bayyana fatan cewa za a kamo waɗanda suka aikata harin domin su fuskanci hukunci.
Wannan hari ya jefa al’ummomin da abin ya shafa cikin alhini, yayin da mazauna yankin suka buƙaci gwamnatin tarayya da ta Jihar Filato su ƙara matakan tsaro a Riyom da sauran yankunan da ke fuskantar hare-hare akai-akai.
Rahotanni sun kuma nuna cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru, yayin da har yanzu mazauna da dama suka bar gidajensu saboda fargabar sake kai wani hari.













