Yau Lahadi, kasashen Amurka, Philippines, Ostiraliya, da sauran kasashe sun fitar da sanarwar hadin gwiwa don “tunawa” da cika shekaru 10 da fitar da hukuncin takkadamar “Philippines da China”, inda ma’aikatar harkokin wajen Sin ta fitar da sanarwa a wannan rana don mayar da martani game da batun.
A cikin sanarwar, ma’aikatar ta bayyana cewa hukuncin takkadamar “Philippines da China”, ya saba wa ka’idoji da dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar MDD kan batun teku, kuma ya sabawa ainihin gaskiyar da ke tattare da batun tekun kudancin Sin, haka kuma ba shi da wata daraja ko amfani.
Ya ce wannan “hukuncin” ba zai yi tasiri ga ikon mallaka da hakkin teku na Sin a kan tekun kudancin kasar ba.
Bugu da kari, game da ikirarin ministan harkokin wajen Japan na cewa kasar tana da hannu a harkokin tekun kudancin Sin, ma’aikatar harkokin wajen Sin ta bayyana cewa duk wani yunkuri na kalubalantar halaltattun hakkoki da muradun Sin, ko kuma lalata zaman lafiya da kwanciyar hankali a tekun kudancin Sin ba zai yi nasara ba. (Safiyah Ma)














