Shugaban Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Duniya (FIFA), Gianni Infantino, ya bayyana cewa hukumar na nazarin yiwuwar ƙara yawan ƙasashen da za su halarci Gasar Kofin Duniya daga 48 zuwa 64 kafin buga gasar shekarar 2030. Wannan na zuwa ne bayan FIFA ta amince a shekarar 2023 da faɗaɗa gasar daga ƙasashe 32 zuwa 48, wanda aka fara aiwatarwa a gasar shekarar 2026.
Da yake zantawa da manema labarai, Infantino ya ce kwamitocin da abin ya shafa za su tattauna wannan shawara bayan kammala gasar Kofin Duniya ta bana. Ya bayyana cewa manufar ita ce a bai wa dukkan yankunan duniya damar samun wakilci mai faɗi, ba wai ƙasashen Turai da na Amurka kaɗai ba. A cewarsa, hakan zai ƙara samar da dama ga ƙasashe masu tasowa su fafata a babban matakin ƙwallon ƙafa na duniya.
Infantino ya ƙara da cewa faɗaɗa gasar zai taimaka wajen bunƙasa wasan ƙwallon ƙafa a ƙasashe masu tasowa, domin idan ba a ba su damar shiga irin wannan babbar gasa ba, ba za su samu ƙwarin gwiwar saka hannun jari da inganta harkar ƙwallon ƙafa a ƙasashensu ba. Ya ce hakan kuma zai ƙara wa gasar armashi da daraja a idon duniya.
Tun daga gasar Faransa ta 1998 zuwa Qatar ta 2022, Kofin Duniya na gudana ne da ƙasashe 32. Sai dai a shekarar 2026 ne aka fara buga gasar da ƙasashe 48, wadda za ta ƙunshi wasanni 104. Ana sa ran gasar Kofin Duniya ta 2030 za a karɓi baƙuncinta a ƙasashe shida da ke nahiyoyi uku, domin bikin cika shekaru 100 da fara gudanar da gasar.












