Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa duk mai niyyar gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027 zai fara biyan Naira miliyan 8.5 a matsayin kuɗin ajiya. Babban Daraktan Hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a shalƙwatar hukumar da ke Kano ranar Lahadi.
Matawalle ya ce an ƙayyade adadin kuɗin ne bayan tattaunawa mai zurfi da nazari domin tabbatar da kyakkyawan shiri da gudanar da aikin Hajji cikin tsari. Ya bayyana cewa hukumar ta tanadi ingantaccen tsarin karɓar kuɗi, inda ya jaddada cewa duk masu niyyar aikin Hajji dole ne su biya kuɗinsu ta banki, sannan su miƙa shaidar biyan ga jami’an cibiyoyin Hajji na ƙananan hukumomi a faɗin jihar.
Babban Daraktan ya buƙaci masu shirin zuwa aikin Hajji su bi hanyoyin biyan kuɗi da gwamnatin Jihar Kano ta amince da su kawai, tare da gargaɗin su da su guji hulɗa da mutane ko ƙungiyoyin da ba su da izini daga hukumar.
Haka kuma ya sanar da cewa an fara sayar da guraben Hajjin 2027 da karɓar kuɗaɗen rajista tun daga Lahadi, 12 ga Yuli, 2026, kuma za a rufe karɓar kuɗin a ranar 26 ga Satumba, 2026.
Matawalle ya buƙaci masu niyyar aikin Hajji da su gaggauta kammala rajista da biyan kuɗinsu domin kauce wa cunkoso a ƙarshen wa’adin da kuma bai wa hukumar damar kammala shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji cikin nasara.













