ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

by Abubakar Sulaiman
13 seconds ago

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta sanar da cewa duk mai niyyar gudanar da aikin Hajjin shekarar 2027 zai fara biyan Naira miliyan 8.5 a matsayin kuɗin ajiya. Babban Daraktan Hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a shalƙwatar hukumar da ke Kano ranar Lahadi.

Matawalle ya ce an ƙayyade adadin kuɗin ne bayan tattaunawa mai zurfi da nazari domin tabbatar da kyakkyawan shiri da gudanar da aikin Hajji cikin tsari. Ya bayyana cewa hukumar ta tanadi ingantaccen tsarin karɓar kuɗi, inda ya jaddada cewa duk masu niyyar aikin Hajji dole ne su biya kuɗinsu ta banki, sannan su miƙa shaidar biyan ga jami’an cibiyoyin Hajji na ƙananan hukumomi a faɗin jihar.

Babban Daraktan ya buƙaci masu shirin zuwa aikin Hajji su bi hanyoyin biyan kuɗi da gwamnatin Jihar Kano ta amince da su kawai, tare da gargaɗin su da su guji hulɗa da mutane ko ƙungiyoyin da ba su da izini daga hukumar.

ADVERTISEMENT

Haka kuma ya sanar da cewa an fara sayar da guraben Hajjin 2027 da karɓar kuɗaɗen rajista tun daga Lahadi, 12 ga Yuli, 2026, kuma za a rufe karɓar kuɗin a ranar 26 ga Satumba, 2026.

Matawalle ya buƙaci masu niyyar aikin Hajji da su gaggauta kammala rajista da biyan kuɗinsu domin kauce wa cunkoso a ƙarshen wa’adin da kuma bai wa hukumar damar kammala shirye-shiryen gudanar da aikin Hajji cikin nasara.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000
  • Abubakar Sulaiman
    Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali
  • Abubakar Sulaiman
    NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus

MASU ALAKA

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara
Manyan Labarai

An Kashe Fitaccen Kwamandan ’Yan Bindiga, Kachalla Sani Yellow A Zamfara

July 12, 2026
inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026

LABARAI MASU NASABA

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sa Miliyan 8.5 A Matsayin Kuɗin Hajjin 2027

July 12, 2026
Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

Atiku Ya Soki Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO Zuwa N50,000

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya

July 12, 2026
Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

Yawan Kwanakin Da Ake Samun Guguwar Rairayi A Kasar Sin Ya Ragu

July 12, 2026
Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

Hukumomin Kasar Sin Sun Tsara Shirin Kandagarkin Ambaliyar Ruwa

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fim ɗin ƙaddara: Anya Ana Samun Irin Wannan ƙaddarar Kuwa?

July 12, 2026
Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

July 12, 2026
‘Lokaci Ya Yi Na Ɗaukar Mataki Kan Masu Yanke Hukunci Da Kansu’

Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

July 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.