Uwargidan Shugaban Ƙasa, Oluremi Tinubu, ta sake tsayawa kan kalamanta da suka janyo ce-ce-ku-ce game da shirin tallafa wa mata ta hanyar sana’ar soya ƙosai, tare da yin kira ga fitattun mawakan Nijeriya irin su Burna Boy da Davido da su yi amfani da dukiyarsu wajen taimaka wa marasa galihu.
Remi Tinubu ta bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin ƙaddamar da Shirin Bankin Abinci na Ƙasa na Al’umma a Lokoja, Jihar Kogi, inda ta sake jaddada goyon bayanta ga shirin Renewed Hope Initiative na tallafa wa jama’a tun daga matakin farko.
Tun a watan Yuni, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta bayyana cewa gwamnati na iya ƙarfafa mata ta hanyar ba su tallafi domin fara ƙananan sana’o’i kamar su soya ƙosai, gasa masara da yin ƙuli-ƙuli.
Sai dai wannan furuci ya haifar da suka daga ɓangarori daban-daban, ciki har da ƙungiyar Ìgbìnmọ́ Májékóbájé Ilé-Yorùbá, fitattun mutane da sauran ’yan Nijeriya, waɗanda suka ce kalaman ba s yi daidai da matsalolin tattalin arzikin da mata ke fuskanta ba.
Ce-ce-ku-ce kan wannan batu ya ci gaba da bin Uwargidan Shugaban Ƙasar, har ma Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi mata da wasa mai kamar barkwanci a wajen liyafar da aka shirya wa ’yan jaridar Fadar Shugaban Ƙasa a Abuja, inda ya kira ta da lakabin “Iya Alakara.”
A lokacin ziyararta Jihar Jigawa a watan Yuni, ta kuma raba tallafin kuɗi na Naira 50,000 ga ƙananan ’yan kasuwa 2,000, tana mai nuna cewa sukar da aka yi ba za ta hana ci gaba da aiwatar da shirin ba.
Maimakon ta janye kalamanta, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta jaddada cewa ƙananan sana’o’i na da mutunci, tana mai cewa masu sayar da barkono, kayan lambu, da kuma masu soya ƙosai na daga cikin mutanen da suka fi cancanta da samun tallafin shirin.













