Gwamnatin Tarayya ta fara gurfanar da sama da mutum 400 da ake zargi da aikata laifukan ta’addanci a gaban alkalan Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Litinin.
Ana gurfanar da waɗanda ake zargin ne a rukuni-rukuni a ɗakunan kotu daban-daban da ke harabar Babbar Kotun Tarayya, yayin da aka dakatar da wasu shari’o’in yau da kullum na ɗan lokaci domin bai wa alkalai damar halartar wannan muhimmin aikin.
Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Lateef Fagbemi, ne ke jagorantar tawagar masu gabatar da ƙara, tare da taimakon Daraktan Gabatar da Ƙararraki na Tarayya, Rotimi Oyedepo.
Waɗanda ake tuhuma na fuskantar laifuffuka daban-daban da suka haɗa da ta’addanci, ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci da kuma taimakawa ko mara wa masu tayar da ƙayar baya baya wajen aikata laifukansu.
Matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na tabbatar da adalci da kuma yaƙi da ayyukan ta’addanci da suka addabi sassa daban-daban na ƙasar nan a shekarun baya-bayan nan.















Discussion about this post