Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar NDC a Jihar Kano, Aminu Abdussalam Gwarzo, ya bayyana Mustapha Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin mataimakinsa a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe a shekarar 2027.
A cikin wata sanarwa da kakakin Kwankwasiyya, Habibu Sale Mailemo, ya fitar, ya ce Mustapha Kwankwaso ne zai kasance mataimakin ɗan takarar gwamna a ƙarƙashin tutar NDC.
Bayyanarsa a matsayin mataimakin ɗan takara na daga cikin muhimman matakan da jam’iyyar ke ɗauka wajen shirye-shiryen ta na zaɓen 2027, kuma ana sa ran hakan zai jawo hankalin masu ruwa da tsaki a siyasar Kano.
Mustapha ɗa ne ga Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ɗaya daga cikin fitattun jiga-jigan siyasa a Arewacin Nijeriya kuma jagoran tafiyar Kwankwasiyya.
Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa fitowar Mustapha Kwankwaso a matsayin mataimakin ɗan takara za ta ƙara wa NDC ƙarfi a matakin ƙasa, musamman a tsakanin magoya bayan Kwankwasiyya da ke da gagarumar kafa a Jihar Kano.















Discussion about this post