An bude taro na 18 na tattaunawa da inganta musaya tsakanin gabobi biyu na mashigin tekun Taiwan, wanda ke kara nuna kudurin babban yankin Sin na hada kan al’ummominta don cimma dunkulewar dukkan yankunanta wuri guda da cimma babban burin raya kasa.
Kasancewar Taiwan wani bangare na Sin ba wani sabon abu ba ne, amma wasu ’yan tsiraru na biye wa rudin masu zugasu, inda suke ganin kamar za su iya ballewa daga babban yankin.
Taron a lardin Fujian, wanda aka fara yinsa tun a shekarar 2009, a bana ya samu halartar adadi mai yawa na wakilai daga dukkan fannoni na yankin Taiwan. Kuma tun bayan kafuwar Fujian matsayin yankin gwaji na inganta raya gabobi biyu na mashigin tekun Taiwan a 2023, an samu nasarori da dama. Misali masu ziyara daga yankin Taiwan a lardin na Fujian ya kai sama da miliyan 1.04 a bara, wanda ya kusa ninka adadin na 2023.
Haka kuma cikin shekaru 3 da suka gabata, sama da sabbin kamfanoni 7,100 masu jarin Taiwan aka kafa a lardin. Shin duk me hakan ke nufi? Wannan ya nuna wa mahukuntan yankin Taiwan da masu ingiza su da ma duniya baki daya cewa, muradun al’ummar Sinawa iri daya ne, kuma burinsu ma haka, watau dunkulewar baki dayan kasar wuri guda da karfafa zumunci da dangantaka a matsayinsu na Sinawa.
Haka kuma, ya nuna cewa jama’ar Taiwan sun aminta da babban yankin wajen kare su da samar musu damarmakin ci gaba. Baya ga kasancewarsa sako mai karfi ga masu tsoma baki cewa, su ne za su ji kunya a duk lokacin da burin dinkewar dukkan yankunan kasar Sin ya tabbata.
Tabbas yadda taron ke samun nasarori ta fuskar inganta mu’amala da musaya, tsakanin jama’ar bangarorin biyu, abun burgewa ne, wanda ke kara nuna kauna da kishinsu ga kasarsu. Tabbas wadannan nasarori na da nasaba da irin hangen nesan babban yankin kasar na karbar bancin wannan taro a duk shekara, wadda alama ce da ke nuna matsayinta na mai sanin ya kamata, wadda ba ta watsi da al’ummarta.
Haka kuma, yunkuri ne da zai kara fahimtar da jama’ar Taiwan kyakyyawar manufar babban yankin game da su. Ko da yake duba da adadin masu ziyara da zuba jari da kafa kamfanoni har ma da mahalarta taron, za mu iya cewa, sun fahimci hakan, sun san kyakkyawar niyyar Sin ta bunkasa ci gaban yankunanta.
Ya kamata mahukuntan Taiwan su gane cewa, yunkurinsu ba zai haifar da komai ba sai karin rashin farin jini da cikas a gare su. Kuma babban yankin kasar Sin shi ne babban mai son ganin ci gaban Taiwan da zaman lafiya da kwanciyar hankalinsa. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post