Gwamnatin Jihar Kano ta ware Naira biliyan 1.5 domin gudanar da shirin auren gata ga ma’aurata 1,500 a faɗin jihar.Babban Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a Kano ranar Litinin, inda ya ce shirye-shiryen gudanar da auren sun yi nisa.
A cewar Daurawa, shirin na daga cikin manyan manufofin jin daɗin al’umma na Gwamna Abba Kabir Yusuf, da nufin rage wa matasa nauyin kuɗaɗen aure tare da ƙarfafa zaman lafiya da kyawawan ɗabi’u a cikin iyali.
Ya bayyana cewa duk masu shirin yin auren an gudanar musu da gwaje-gwajen lafiya na wajibi, waɗanda suka haɗa da gwajin cutar HIV/AIDS, hanta (Hepatitis), dacewar ƙwayoyin halitta (genotype) da kuma gwajin juna-biyu, domin tabbatar da cewa auren ya kasance mai ɗorewa da ingantacciyar lafiya.
Daurawa ya ƙara da cewa kowanne ma’aurata zai karɓi tallafin kayan gida da darajarsu ta kai Naira miliyan 1, wanda ya haɗa da Katifa da gadon kwana, Zanen gado, Matashin kai, Kabad (wardrobe), Kayan abinci da sauran kayan amfanin gida.
Ya ce shirin na nufin taimaka wa sabbin ma’aurata su fara rayuwar aure cikin sauƙi da walwala, tare da rage matsalolin tattalin arziki da ke hana matasa yin aure.















Discussion about this post