‘Yan Bindiga Mako biyu da suka wuce, wasan kwaikwayo ya faru tsakanin jami’an tsaro da ‘yan bindiga a arewa maso yamma har ya yi sanadiyyar rasa wani mutum mai daraja, yayin da matar tsohon jami’in soja har yanzu tana hannun ‘yan ta’adda.
A baya dai, jami’in sojan shi ne mai magana da yawun rundunar tsaro ta Nijeriya.A ranar 30 ga Mayu, Mejo Janar Rabe Abubakar (mai ritaya), tare da matarsa an yi garkuwa da su a karamar hukumar Matazu ta Jihar Katsina.
Yayin da labarin garkuwan ya ta’allaka ne a kan ayyukan laifukan ‘yan fashin daji, lokacin da suka farauci Janar Abubakar, matarsa da ‘ya’yansa galibi ba su fito a rahotannin labarai ba.
Janar Abubakar da matarsa Amina Abubakar, suna kan hanyarsu zuwa bikin aure ne lokacin da ‘yan bindiga suka yi masu kantar bauna a kan hanyar Marabar Musawa-Kafinsoli suka yi garkuwa da su zuwa cikin daji da ke kusa.
daya daga cikin ‘ya’yan ma’auratan, Khadijah, ta yi aure ne watanni takwas da suka wuce a Kaduna.
A yanzu haka dai, ‘yan fashi suna amfani da matan tsohon jami’in a matsayin hanyar isar da bukatu da sako ga hukumomi.A cikin wani sabon bidiyo da aka sanya a kafafen sada zumunta, an ga tana rokon gwamnatin jiha da ta cika bukatun ‘yan bindigar.
Yayin garkuwan, direban ma’auratan, Abdullahi Sa’idu, wanda sunansa ma ba a fi magana a kansa ba, ya ji rauni daga harbin bindiga amma ba a yi garkuwa da shi ba.














Discussion about this post