Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na kan turbar neman ci gaba ta hanyar lumana, kuma tana gina karfin sojinta ne da nufin kare ikon mulkin kai, da tsaron kasa da cimma nasarar bunkasa kai.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan a Litinin din nan, yayin taron manema labarai na yau da kullum da aka saba gudanarwa, lokacin da yake tsokaci kan wani rahoto mai nasaba da ci gaban da rundunar sojojin kasar Sin ke samu, ya ce rahotanni da dama sun rika zargin kasar Sin da kokarin aiwatar da babakere.
To sai dai kuma hakan matukar kuskure ne. Ya ce bunkasar rundunar sojin kasar Sin na nufin karin karfi domin wanzar da zaman lafiya a duniya.
Don haka, Lin Jian ya yi kira ga bangarorin da batun ya shafa da su dakatar da furta zargin cewa wai “Sin barazana ce”, su kuma yi cudanya da Sin bisa hahikanin halinta da sanin ya kamata. (Saminu Alhassan)















Discussion about this post