Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta yabawa gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, bisa ƙarfafa Ilimin Fasaha da Horon Sana’o’i a jihar, bayan kammala horar da kusan ɗalibai 3,000 daga cibiyoyin koyon sana’o’i guda tara da ke faɗin jihar.
Yabon ya fito ne a cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Lahadi, wadda Boriowo Folasade, Daraktar Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a ta Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, ta sanya wa hannu.
A cewar sanarwar, Ministan Ilimi, Maruf Tunji Alausa, ya bayyana wannan shiri a matsayin babban mataki na ƙarfafa matasan Nijeriya ta hanyar ba su ƙwarewa masu amfani da za su iya samun aikin yi da su.
Ministan ya ce: “Wannan shiri da Gwamna Zulum ya ƙaddamar babban mataki ne na bai wa matasan Nijeriya ƙwarewa ta aiki da za su iya dogaro da ita wajen samun abin yi.”















Discussion about this post