Wani mutum mai shekaru 45, mai suna Auwalu Adamu, ya rasu bayan da ake zargin sabuwar matarsa ta biyu, Khadija Sulaiman, ta caka masa wuƙa, watanni biyu kacal bayan aurensu a unguwar Hayin Lawali da ke ƙaramar hukumar Ungogo a Jihar Kano.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ranar Lahadi bayan wata zazzafar muhawara da ta kaure tsakanin ma’auratan a gidansu.
Mazauna yankin sun bayyana cewa tun bayan auren nasu, zaman bai yi daɗi ba, domin ana yawan samun saɓani da rigingimu a tsakaninsu, waɗanda galibi kan zama abin magana a cikin al’umma.
Wani maƙwabci da ya nemi a sakaya sunansa ya ce mamacin ya fito daga gidan da gudu bayan ya samu mummunan raunin wuƙa a wuyansa, kafin daga bisani ya faɗi ƙasa.
Wani mazaunin yankin kuma ya ce yawan faɗace-faɗacen ma’auratan ya kasance abin damuwa ga al’ummar yankin tun kafin aukuwar lamarin.
Shugaban wata ƙungiyar tsaron al’umma a yankin, Nazifi Abdullahi, ya ce bayan faruwar lamarin, matar ta yi yunƙurin tserewa, amma wasu mata maƙwabta sun hana ta guduwa har zuwa lokacin da jami’an ‘yansanda suka isa wurin.
Ya zuwa lokacin da ake tattara wannan rahoto, rundunar ‘yansandan Jihar Kano ba ta fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.














Discussion about this post