Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Katsina ta yanke wa wata mata mai suna Hauwa’u Mukhtar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ta same ta da laifin aikata laifuka masu alaƙa da ta’addanci.
An same ta da laifi ne kan tuhume-tuhume guda biyu da suka haɗa da haɗa baki domin aikata ta’addanci da kuma taimakawa tare da ba da goyon baya ga ayyukan ta’addanci.
Jami’an DSS ne suka kama Hauwa’u a ranar 16 ga Satumban 2023 a tashar mota ta Jibia da ke Jihar Katsina, inda ake zargin tana ƙoƙarin kai alburusai ga wani shugaban ’yan bindiga mai suna Ado da ke aikata ta’addanci a yankin dazukan Dunburum.
Yayin yanke hukunci, Mai Shari’a A.B. Bawale ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun tabbatar da tuhume-tuhumen da ake yi wa wadda ake ƙara ba tare da wata shakka ba, ta hanyar hujjoji, kayayyakin da aka gabatar a kotu da kuma shaidun da aka bayar yayin shari’ar.
Saboda haka, kotun ta same ta da laifi a kan dukkan tuhume-tuhumen biyu tare da yanke mata hukuncin kisa ta hanyar rataya, bisa tanade-tanaden Dokar Penal Code ta Jihar Katsina ta shekarar 2021.
Hukuncin ya zo ne a daidai lokacin da hukumomin tsaro ke ci gaba da ƙoƙarin dakile ayyukan ’yan bindiga da masu ta’addanci a sassan Arewa maso Yammacin Nijeriya.














Discussion about this post