Dakarun rundunar sojin Nijeriya sun yi nasarar ceto wasu mutum huɗu da aka yi garkuwa da su yayin ci gaba da farmakin da ake kai wa kan wani fitaccen shugaban ’yan bindiga, Kachalla Muhammadu Fulani, da mabiyansa a Jihar Katsina.
An bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Kwamishinan Harkokin Tsaro da Cikin Gida na Jihar Katsina, Dr. Nasir Mu’azu, ya sanya wa hannu kuma aka fitar da ita da safiyar Laraba.
Rahotanni sun nuna cewa mutanen da aka ceto sun kasance cikin waɗanda aka yi garkuwa da su tare da tsohon Daraktan Yaɗa Labarai na Hedikwatar Tsaro ta Ƙasa (DDI), Marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar mai ritaya, wanda ya rasu yayin da yake hannun masu garkuwa da mutane.
Tun da farko, dakarun soji sun ceto matar marigayin, Hajiya Amina Abubakar, kafin wannan sabon samame da ya kai ga kuɓutar da sauran waɗanda suka rage.
A cewar gwamnatin jihar, waɗanda aka ceto sun haɗa da Musa Yakuba, mai shekaru 62; Alhaji Sa’adu Dayi, mai shekaru 68; Mukhtar Danja, mai shekaru 36, da Salisu Danja, mai shekaru 50.
Sanarwar ta ce an kuɓutar da su ne a yayin ci gaba da ayyukan soji a wuraren da ake zargin ’yan bindigar na fakewa da gudanar da ayyukansu.
Gwamnatin Jihar Katsina ta yaba wa jami’an tsaro kan ƙoƙarin da suke yi wajen yaƙi da ’yan bindiga tare da tabbatar da cewa za a ci gaba da ɗaukar matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.













Discussion about this post