Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja ta bayar da umarnin dakatar da aiwatar da hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta yanke, wanda ya umarci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta soke rajistar jam’iyyar ADC da wasu jam’iyyun siyasa huɗu.
Kotun ta umarci INEC da kada ta aiwatar da umarnin soke rajistar jam’iyyun har sai an kammala sauraron ƙarar da jam’iyyun da abin ya shafa suka shigar domin ƙalubalantar hukuncin Babbar Kotun Tarayya.
A ranar Litinin, Mai Shari’a Peter Lifu na Babbar Kotun Tarayya ya umarci INEC ta soke rajistar jam’iyyun ADC, Accord Party da wasu jam’iyyu uku bisa zargin kasa cika wasu sharuɗɗan kundin tsarin mulki da dokokin zaɓe suka tanada domin ci gaba da kasancewa a matsayin jam’iyyun siyasa masu rijista.
Sai dai kwamitin alkalai uku na Kotun Ɗaukaka Ƙara ya soki hukuncin da aka yanke, inda ya bayyana matakin da kotun tarayya ta ɗauka a matsayin rashin mutunta kotun da ta fi ta girma da kuma abin da ya saɓa wa tsarin shari’a.
Saboda haka, jam’iyyun da abin ya shafa za su ci gaba da kasancewa a matsayin halastattun jam’iyyun siyasa har sai an yanke hukunci na ƙarshe kan shari’ar da ke gaban kotu.














Discussion about this post