Tawagar mata ta Nijeriya ‘yan ƙasa da shekaru 20, Falconets, ta samu gurbin zuwa matakin kwata-fainal na gasar cin kofin duniya ta FIFA U-20 bayan ta doke Ingila da ci 3-0 a wasan da suka fafata ranar Alhamis a filin wasa na Bielsko-Biala, da ke ƙasar Poland.
Tosin Rafiu ce ta fara jefa wa Nijeriya ƙwallo a minti na bakwai da fara wasan, kafin Ingila ta samu damar ramawa ta hanyar bugun daga kai sai mai tsaron gida a minti na 33.
Sai dai mai tsaron ragar Nijeriya, Christiana Uzoma, ta tare bugun Rachel Maltby, inda ta hana Ingila damar zura ƙwallo.
Bayan dawowa daga hutun rabin lokaci, Falconets ta ƙara zura ƙwallo ta biyu bayan mintuna biyu, kafin Mary Mamudu ta ci ta uku a minti na 73.
Nasarar ta tabbatar wa Nijeriya samun gurbi a matakin kwata-fainal, inda za ta kara da wadda ta yi nasara a wasan zagayen ‘yan 16 tsakanin Poland da Colombia.














