A yau Alhamis aka bude bikin baje koli na 23 na Sin da ASEAN da taron tattauna kasuwanci da zuba jari na bangarorin biyu, a birnin Nanning na lardin Guangxi na Sin.
Mamban kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS, kuma mataimakin firaministan kasar Sin Ding Xuexiang ya halarci bikin tare da gabatar da jawabi.
A cewar Ding Xuexiang, bayan aiwatar da tsarin daukaka yankin ciniki cikin ‘yanci na Sin da ASEAN na 3.0, zai kara ingiza sabon kuzari ga bunkasar tattalin arzikin yankin. Ya kuma gabatar da shawarwarin gina yankin ciniki cikin ‘yancin na Sin da ASEAN a babban mataki.
Bayan bikin bude baje kolin, ya kuma gana da shugabannin siyasa daga kasashen Myanmar da Vietnam da Laos, wadanda ke halartar taron. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha)














